Monday, 14 March 2022

RUBUTU NA 5: TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20 | تاريخ القراء العشرة ورواتهم

  قِرَاءَةُ الإِمَام ابن كَثِيرٍ المَكي

TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20
تاريخ القراء العشرة ورواتهم
RUBUTU NA: 5️⃣
Rubutawar
✍Habibu Muhammad shugaba
Yau kuma Zamuyi bayani ne akan Qira'ar AL-IMAM IBN KATHIR insha Allah
ABUBUWAN DA KE KARKASHIN WANNAN RUBUTUN
👇👇👇👇👇
1- WANENE AL-IMAM IBN KATHIR
2- MALUMAN AL-IMAM IBN KATHIR
3- DALIBAN AL-IMAM IBN KATHIR
4- BAYANI AKAN QIRA'AR IBN KATHIR
1- WANENE AL-IMAM IBN KATHIR
SUNANSHI Abdullahi ibn Kathir ibn Amr ibn Abdullahi Ibn Zazan ibn Fairuzan ibn Hurmuz Almakky Addariyyu.
ALKUNYARSHI: Abu Ma'abad
An haifi Al-imam ibn kathir a garin Makkah a shekara ta 45 bayan Hijrah
Sai dai abunda ya Kamata Mu Sani a nan shine
Wannan ibn kathir din ba shine mai Tafsir ba wanda akafi sani mai تفسير ابن كثير
Shi wannan Abdullahi ibn Kathir ne sunanshi an haifeshi a shekara ta 45 bayan Hijrah ya rasu a shekara ta 120 bayan Hijrah
Shi kuma wancen Isma'il ibn kathir an haifeshi Garin Basra a shekara ta 701 bayan Hijrah ya rasu Dimashqa ta Sham a shekara ta 774 bayan Hijrah
Yanada Kyau mu kula
Al-imam ibn kathir ya Hadu da wasu daga Cikin Sahabbban Annabi صلى الله عليه وسلم
Daga cikin wadanda ya hadu dasu akwai
1- Abdullahi ibn Al-zubair رضي الله عنهما
2- Abu Ayyubal ansary رضي الله عنه
3- Anas ibn Malik رضي الله عنه
Haka kuma Ya Hadu da Tabi'ai Kamar
1- Mujahid ibn jabr
2- Dirbas Maula ibn Abbas رضي الله عنهما
3- Abdullahi ibn Assa'ib Al-makhzumy
Al-imam ibn kathir shine Shugaban Makaranta Qur'ani a garin Makkah a zamaninshi
Ibn kathir ya kasance Dogo ne mai Farin Gemu اللحية
Ya kasance mai Fasaha Masanin ilimin Balagah
2- MALAMAN AL-IMAM IBN KATHIR
Tabi'ai sune Malaman ibn kathir Duk da cewa yaga wasu daga cikin sahabbai Kasancewar an haifeshi a lokacin da Hijrah takeda shekaru 45
Daga cikin malaman shi akwai
1- Abdullahi bn Assa'ib shi kuma Abdullahi bn Assa'ib yayi karatu ga Sahabbai biyu
- Sayyidina Ubayyu bn Ka'ab رضي الله عنه
- Sayyidina Umar bn Alkhaddab رضي الله عنه
2- Mujahid ibn Jabr shi kuma mujahid yayi karatu ga Abdullahi ibn Al-sa'ib da kuma Abdullahi ibn Abbas رضي الله عنهما
3- yayi karatu ga Dirbas Maula ibn Abbas رضي الله عنهما Shi kuma Dirbas Yayi Karatu ga Maulanshi Abdullahi ibn Abbas رضي الله عنهما
Shi kuma Abdullahi ibn Abbas Yayi Karatu Ga Ubayyu ibn Ka'ab da Zaid ibn Sabit رضي الله عنهم
Su kuma
1- Umar bn Alkhaddab رضي الله عنه
2- Ubayyu bn Ka'ab رضي الله عنه
3- Zaid ibn Sabit رضي الله عنه
Sunyi Karatu Ga Annabi muhammad صلى الله عليه وسلم
3- DALIBAN AL-IMAM IBN KATHIR
Al-imam ibn kathir yanada Dalibai masu Tarin yawa kuma wadannan daliban jigajigai ne a wajen neman Ilimi da kuma yadashi Duniyar ilimi ta yadda da cewa malamai ne su
Rubutun mu bazai isa mu kawo sunayen su da yawa ba amma ga wasu daga cikin su
1- Isma'il ibn Abdullahi Alqusd
2- Isma'il ibn muslim
4- Hammad ibn Salamah ( masanin Hadisi)
5- Hammad ibn Zaid ( masanin Hadisi)
6- Sulaiman ibn Almugirah
7- Alkhalil ibn Ahmad ( Masanin ilimin Larabci)
8- Shibl ibn Abbad
9- Sadawatu ibn Abdullahi ibn Kathir (danshi)
10- Abdulmalik ibn juraij Almakky
11- Aliyu ibn Alhakam
12- Mudartif ibn Ma'aQil
13- Abu Amr ibn Al-ala' Albasry ( Daya Daga cikin Qurra'u saba'ah)
14- Ibn Abi Mulaikah
15- Sufyan ibn Uyainah (masanin Hadisi)
16- Harun ibn musa
Da dai Sauransu
AL-ASMA'I YACE : Nace da Abu Amr Albasry : Kayi karatu ga ibn kathir? Sai yace : Eh Nayi Khatama ( Sauka) ga ibn Kathir bayan Nayi Sauka Ga mujahid, Ibn kathir ya kasance mafi sanin ilimin larabci fiye da mujahid.
MUJAHID YACE : ibn kathir bai Gushe ba A matsayin imami Jagora a fannin karatun Qurani a garin makkah ba Har lokacin da ya Rasu a shekara ta 120 bayan Hijrah.
SUFYAN IBN UYAINAH YACE: na Halarci Janazar ibn kathir Addary A shekara ta 120 bayan Hijrah
Ibn kathir ya rasu a shekara ta 120 bayan Hijrah
Yanada Shekara 75 a rayuwar shi
رحمه الله رحمة واسعة
4- BAYANI AKAN QIRA'AR IBN KATHIR
Qira'ar ibn Kathir Qira'a ce aingantatta Mutawatirah Har Zuwa Ga Annabi صلى الله عليه وسلم kuma Dayace Daga cikin Qira'o'i 7
Qira'ar ibn kathir haka take Kamar Sauran Qira'o'i Tanada Riwayoyi biyu
- Riwayar Bazzy an ibn kathir
- Riwayar Qumbul an ibn kathir
KAFIN MU SHIGA BAYANI AKAN WANNAN QIRA'AR
GA WANI BAYANI MAI MUHIMMANCI DA YA KAMATA MU SANI
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇
mu sani cewa Bazzy da Qumbul Basuyi Karatu Kaitsaye (Baki da baki) Ga ibn kathir ba
Akwai mutane a tsakaninsu da ibn kathir
Koda ibn Kathir ya rasu baa ma Haifesu ba
Saboda ibn kathir ya rasu a shekara ta 120
An haifi Bazzi a shekara ta 170
An haifi Qumbul a shekara ta 195
Nayi bayani a rubutu na na farko cewa
Wadanda ake Jinginawa riwayoyi (Masu Riwaya) Sun kasu gida uku
1- akwai wadanda sukayi karatu baki da baki ga QARI'AI da ake jinginawa riwayarsu zuwa garesu kamar
Qalun da warsh sunyi karatu baki da baki ga Nafi'u
2- Akwai wadanda A tsakaninsu da QARI'AN akwai wasidar Mutun Daya kamar
- Dury da susi Sunyi karatu ga Yahyal Yazidiyyi shi kuma yahya yayi karatu ga Abu amr
-Kamar Khalaf da khallad Sunyi karatu ga Sulaim shi kuma sulaim Yayi Karatu Ga Hamzah
3- Akwai wadanda akwai fiye da mutun daya a tsakaninsu da QARI'IN DA sukayi riwaya a gareshi kamar Bazzi da Qumbul basuyi karatu kai tsaye ga ibn kathir ba Akwai fiye da mutun daya a tsakanin su
Abun da yasa hakan ta faru shine
A lokacin da wannan ilimin na riwayoyi yayi yawa ya fadada riwayoyin sunyi yawa Kasancewar kowane Qari'i yanada dalibai masu dinbin yawa kuma kowane yana jingina riwayar shi zuwaga wannan Qariin
Sai akayi niyyar Takaita Riwayoyin Akace kowane QARI'I zaa fitar da mutun biyu daga cikin Rawiyanshi (Dalibanshi) Wadanda sukafi kwarewa da kuma tsoron Allah Da tsantseni domin a jingina riwayar shi zuwa garesu
Sai a bincika Idan an samu wanda ya cika sharudan daga cikin Daliban QARI'IN to الحمد لله idan kuma baa samu ba sai a duba cikin Daliban daliban QARI'IN haka kuwa akayi har Zabin Yazo Ga Bazzi da Qumbul Da ire irensu
Wannan shine Maanar Fadar Shadibiyy
تَخَيرَهم نُقَّادُهُم كلَّ بَارِعٍ
وَلَيسَ عَلى قُرءَانِه مُتَأَكِّلا
Wannan QIRA'AR Tanada Ayoyi 6220 Dubu shida da dari biyu da Ashirin
Wannan Adadin Na Ganshi ne a mushafin da nike dashi Na QIRA'AR IBN KATHIR 6220
Sai dai kuma Naga wani Adadin da ya sabawa wannan Adadin a wani littafi na QIRA'AR IBN KATHIR
Sunce Adadin Ayoyin Qira'ar ibn kathir sune 6210 dubu shida da dari biyu da goma
Wannan adadin shine Adadin da Abu Amr Addany ya riwaito Da sanadinshi Zuwa ga ibn kathir shi kuma ibn kathir ya Riwaito shi zuwa Ga mujahid ibn Jabr shi kuma mujahid Daga Abdullahi ibn Abbas رضي الله عنهما shi kuma Ibn Abbas Daga Ubayyu Ibn ka'ab رضي الله عنه
QIRA'AR IBN KATHIR
Zamuyi bayani ne kawai ga kalmomin Da ibn kathir ya kebanta dasu wadanda ya sabawa sauran QIRA'O'I wurin karanta su Sauran Bayani kuma Zamuyi shi a wurin bayani da zamuyi na musamman gameda wadannan riwayoyi nashi (Bazzy da Qumbul) A rubutun da zamuyi na Gaba insha Allah
Yadda Na Rubutasu haka ibn kathir ke karantawa sabanin sauran Qira'o'i
👇👇👇👇👇👇👇
1- وَاللَّذَآ نِّ يأتيانها منكم
Da yin madda wurin ذ da shadda ga ن
2- القُدْس
Da yin Skun ga harafin دْ a wannan kalmar duk inda tazo cikin Qurani
3- قل إن الله قادر على أن يُنزِلَ ءاية
A wannan ayar shi kadai ke karantawa haka يُنزِلَ da cire shadda
4- يجعل صدره ضَيْقًا da kuma ضَيْقًا مقرنين دعوا هنالك
Yana karantasu da cire shadda ga ي tareda daureta
5- فتلقى ءَادَمَ من ربه كَلِمَـٰتٍ
Kamar yadda na rubuta haka yake karantawa ءَادَمَ da kuma كَلِمَـٰتٍ
6- وما ربك بغـٰفل عما يَعْمَلُونَ () أفتطمعون
Yana sa ي wurin يَعْمَلُونَ Wacce daga ita sai أفتطمعون
7- جَبْرِيلَ
Duk ida tazo a Qur'ani kamar haka جَبْرِيلَ
8- إذا سلمتم ما أَتَيْتُم بالمعروف
Da cire madda wurin ءَاتَيْتُم sai ya dawo أَتَيْتُم
9- وما أَتَيْتُم من ربا ليربوا في أموال الناس
Da cire madda wurin ءَاتَيْتُم sai ya dawo أَتَيْتُم
10- أَأن يُؤْتَى أحد مثل ما أوتيتم
Da kara harafin أ a wannan kalmar ( kar mu manta da Tashilin da yakeyi idan an samu hamza biyu a cikin kalma daya kamar haka)
11- وَكَآئِن
A duk inda kalmar وَكَأَيِّن tazo to yana karantata وَكَآئِن da yin maddar ك da musanya ي zuwa ء
12- كأنما يَصْعَدُ في السماء
Da daure ص da cire shadda kamar yadda na rubuta
13- وأعد لهم جنـت تجرى مِن تَحْتِهَا الأنهـر خـلدين أبدا ( سورة التوبة)
Yana kara harafin مِن a wannan ayar yayiwa تِ kasra cikin ayar والسابقون الأولون dake taubah
14- لقد كان في يوسف وإخوته ءَايَتٌ للسائلين
Da cire madda wurin ءَايَــٰتٌ sai ya karanta ءَايَتٌ babu madda
15- وقالت هَيْتُ لك
Da yiwa ه fat'ha da yiwa ت damma
16- وكذلك مكنا ليوسف في الأرض يتبوأ منها حيث نَشَآء
Da sanya ن wurin ي kamar yadda na Rubuta نَشَآء
17- لقالون إنما سُكِرَتْ أبصارنا
Da cire shadda Ga harafin ك
18- قال أبشرتموني على أن مسني الكبر فبم تُبَشِّرُوٓنِّ
Da yin madda ga ر tareda yiwa ن shadda da kuma karsra تُبَشِّرُوٓنِّ
19- ولا تك في ضِيقٍ( سورة النحل ) da kuma ولا تكن في ضِيقٍ (سورة النمل )
Da yin kasra ga ض kamar yadda na rubuta ضِيقٍ
20- إن قتلهم كان خِطَآءً كبيرا
Da yiwa خ kasra da maddar ط kamar yadda na rubuta خِطَآءً
21- قال ما مَكَّنَنِي فيه ربي خير
Da kara harafin ن da kuma cire shadda مَكَّنَنِي
22- أي الفريقين خير مُّقَامًا وأحسن نديا
Yin dwamma ga harafin م kamar yadda na rubuta مُّقَامًا
23- قالوا إن هَذَآنِّ لسـحران
Da yin maddar ذ da kuma shadda ga ن kamar yadda na Rubuta هَذَآنِّ
24- فلا يَخَفْ ظلما
Da cire madda wurin خ kamar yadda na Rubuta يَخَفْ
25- أَلَمْ يرى الذين كفروا أن السموت والأرض كانتا رتقا
Da cire harafin و asalinshi أولم sai ya karanta أَلَمْ
26- هَذَآنِّ خصمان اختصموا في ربهم
Da yin maddar ذ da kuma shadda ga ن kamar yadda na Rubuta هَذَآنِّ
27- والذين هم لأَمَــٰــنَتِهِم وعهدهم راعون (سورة المؤمنون ) da kuma (سورة المعارج)
Da cire madda wurin harafin ن
28- ولا تأخذكم بهما رَأَفَةٌ في دين الله
Da yiwa أ fataha
29- ظُلُمَــٰتٍ بعضها فوق بعض
Da yin kasrataini wurin ت ظُلُمَــٰتٍ
30- وَنُنزِلُ المَلَئكَةَ تنزيلا
Cire wasali ga ن Da yin dwamma ga ل da fatahar ةَ kamar yadda na Rubuta
31- وهو الذى أرسل الرِّيحَ نشرا بين يدي رحمته
Da yin Tauhidi ga kalmar الرِّيحَ kamar yadda na rubuta ta
32- أو لَيَأْتِيَنَّنِي بسلطـن مبين
Da kara harafin ن wurin kalmar لَيَأْتِيَنَّنِي
33- فإنك لا تسمع الموتى ولا يَسْمَعُ الصُّمَ الدعاء
Yana karanta wadannan kalomomin haka kamar yadda na Rubuta su يَسْمَعُ الصُّمَ a cikin suratu Namli
34- قال إني أريد أن أنكحك إحدى ابنتي هَــٰــتَــيٰٓـــنِّ على أن تأجرني ثماني حجج
Da yin Madda wurin harafin ت da kuma yin shadda Ga ن kamar haka هَــٰــتَــيٰٓـــنِّ
35- قَالَ ربي أعلم بمن جاء بالهدى من عنده
Yana cire Harafin و dake farkon wannan ayar وَقَالَ sai ya karanta قَالَ kawai
36- يَــٰــبُــنَـيْ لا تشرك بالله da kuma يَــٰــبُــنَـيْ إنها إن تك مثقال حبة
Yana maranta يَــٰــبُــنَـي din da sukazo a cikin wadannan ayoyin Da daure harafin ي يَــٰــبُــنَـيْ wadannan ayoyin kawai 2 da na rubuta
37- واذكر عَبْدَنَا إبراهيم وإسحــق ويعقوب أرلى الأيدي والأبصـر
Yana karanta kalma عِبَــٰـدَنا da fataha ga ع tareda ciremishi madda da daure ب kamar haka عَبْدَنَا
38- كذلك يُوحَى إليك وإلى الذين من قبلك الله
Da yin fat'ha ga harafin ح kamar haka يُوحَى
39- فيها أنهـٰـر من ماء غير أَسِنٍ
Yana karantawa da cire madda ga harafin أ kamar haka أَسِنٍ
40- والله بصير بما يَعْمَلُونَ
Yana saka ي wurin harafin ت a karshen سورة الحجرات aya ta kashe
41- هذا ما يُوعَدُونَ لكل أواب حفيظ
Yana saka ي wurin harafin ت a wannan kalmar يُوعَدُونَ
42- وَمَنَــوٰٓءَةَ الثالثة الأخرى
Yana kara ء da kuma madda ga wannan kalmar kamar yadda na rubuta ta وَمَنَــوٰٓءَةَ
43- يوم يدع الداع إلى شيء نُّكْرٍ
Shi kadai ke daure Harafin كْ a wannan ayar نُّكْرٍ
44- يرسل عليكما شِوَاظٌ من نار
Shi kadai keyin kasra ga harafin ش a wannan ayar شِوَاظٌ
45- نحن قَدَرْنَا بينكم الموت
Yana cire shadda Ga harafin د a cikin wannan surar Waki'ah قَدَرْنَا
46- تبت يدا أبي لَهْبٍ وتب
Yana daure Harafin ه a wannan Kalmar لَهْبٍ
WADANNAN sune kalmomin da ibn kathir ya sa6awa kowa daga cikin Qurra'u a garesu kar mu manta kalominda nayiwa WASALI su nike nufi kuma yadda na rubutasu
إن شاء الله
Nan Zamu tsaya a wannan rubutun sai Ku Yi kokari ku samu sauran rubutun da mukayi a baya da kuma wadanda zamuyi nan gaba idan Allah ya Kaimu
JAN HANKALI
👇👇👇👇
Duk wanda Zaiyi sharing ko Kwafi Na wannan Rubutun nawa To ya yi Sharing Dinshi A yadda Na Rubutashi Kar ya kara komai kuma Kar ya canja komai abar shi yadda nayishi
Duk wanda yakeda Ta'aliki ko gyara Ko shawara ko Mulahaza akan Wannan Rubutun to ya atuntubeni nizan gyara Da kaina Amma Kar A canja Min rubutu.
Ga lambar da zaa tuntubeni da ita +2348034468543
✍️WANDA YA RUBUTA
Habibu Muhammad Shugaba
+2348034468543
Monday
17-11-1442
28-06-2021

RUBUTU NA 4: TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20 | تاريخ القراء العشرة ورواتهم

 TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20

تاريخ القراء العشرة ورواتهم
وايةُ وَرشٍ
عَن الإِمَامِ نَافع المَدَني
RUBUTU NA: 4️⃣
Rubutawar
✍Habibu Muhammad shugaba
ABUBUWAN DA KE KARKASHIN WANNAN RUBUTUN
👇👇👇👇👇
1-Wanene warsh
2-Daliban warsh
3- Takaitaccen bayani Akan Usul Na Riwayar Warsh ( Abubuwan da Aka gina Riwayar akansu)
1- WANENE WARSH
SUNANSHI:- Usman ibn Sa'id, ibn Abdullahi, ibn Amr, ibn Sulaiman, ibn Ibrahim,
Wasu Kuma Sunce SUNANSHI:- Usman ibn Sa'id Adiyyi ibn Gazwan ibn Dawud ibn Sabiq
LAQABINSHI :- Warsh
ALKUNYARSHI :- Abu Sa'id ko kuma Abul-qasim
Warshu Mutumin Misra Ne
An haifeshi a shekara ta 110 bayan Hijrah a misra
Ya rasu a misra a shekara ta 197 yanada shekara 87 a duniya رحمه الله
Shine shugaban masu Karatun Qur'anida karantar dashi a kasar misra a zamanin shi
A shekara ta 155 bayan Hijrah Warsh ya zo Garin Madinah Domin yayi karatu a wurin Malaminshi Nafi'u
Kuma yayi Saukar Qur'ani a wurin Nafi'u Adadi masu yawa
Ance Al-imam Nafi'u ne ya Yiwa Warshu Lakabi da WARASHAN ( وَرَشَان) ana karantashi da yiwa harafin وَ da رَ da شَ fataha وَرَشَان
Nafi'u Ya kasance idan Zai kirashi yakan ce dashi " zo yakai WARASHAN"
Ko kuma idan Yanaso warshu ya Karanta Qurani sai yace dashi " karanta yakai WARASHAN"
Ko kuma idan Yana nemanshi yace " ina WARASHAN?"
Daga baya sai aka Mayar Dashi WARSH وَرْشُ
Daga baya sunan ya kasance dashi ne aka san Warshu ba asalin Sunanshi (Usman) ba
Sunan Warshu ya kasance suna mafi soyuwa a wurin Warshu Har ya kasance yana Cewa malamina ne yayimin wannan lakabi (Warsh)
Ance Warshu ya kasance yanada Fari (hasken fata) wannan ne yasa Nafi'u ya yimishi Laqabi da Warsh saboda kalmar WARSH Kalma ce da take nuni akan Wani abu da akeyi Da NONO اللبن Sai akayiwa warshu laqabi dashi Saboda Hasken fatar shi
Wasu kuma sunce Warsh ya kasance Kajere( Guntu) bayada tsayi saboda haka yake saka Tufafi Gajeru wadanda har kafafuwanshi (kwaurinsh) suna bayyana Wannan ne Yasa Akayimishi Lakabi Da Warsh
2- DALIBAN WARSH
Warsh yanada Daliban da yawa Zamu kawo wasu daga cikinshu
1- yunus ibn abdul-A'ala
2- Abu ya'akubal Azraq
3- Abu mas'ud Al-aswadullaun
4- Ahmad ibn Salih
5- Dawud ibn Abi Daybab
6- Aburrabi'i Sulaiman ibn Dawud Al-mahdi
7- muhammad ibn Abdullahi ibn yazid Almakky
8- abdussamad ibn Abdulrahman ibn Alqasim
9- Amr ibn Basshar
10- Amir ibn Sa'id Abul-ash'as
Da sauransu
3- TAKAITACCEN BAYANI AKAN RIWAYAR WARSH
Riwayar Warsh Daya ce daga cikin Riwayoyi 20 ingantattu daga cikin Riwayoyin Qurani mai Girma
Kuma Tana daya Daga cikin Riwayoyi 4 da sukafi sauran Riwayoyi karbuwa a duniyar mu ta yanzu
sune:-
1- Riwayar hafs
2- Riwayar Warsh
3-Riwayar Qalun
4- Riwayar Dury an abi Amr
Haka Kuma Riwayar Warsh Riwaya ce ingantatta wacce takeda INGANTACCEN sanadi tun daga Warsh Har zuwa Ga manzo Allah صلى الله عليه وسلم
Ga Isnadin Riwayar Warsh
Wanna RIWAYA ce da warsh ya Riwaito daga malaminshi Nafi'u ibn Abdulrahman ibn Abi nu'aim Almadany, shi kuma Nafi'u yayi karatu Ga Malumanshi :-
1- Abu ja'afar Almadany
2- Abu Dawud Abdulrahman ibn Hurmzu Al-a'araj
3- Shaibah ibn nisah Al-qady
4- Abu Abdullahi muslim ibn jundub Alhuzaly
5- Abu Rauh Yazid ibn Ruman
Su kuma wadannan maluman na Nafi'u su 5 sunyi karatu Ga Sayyidina Abu Hurairah رضي الله عنه da Abdullahi ibn Abbas رضي الله عنهما Da Abdullahi bn Ayyash ibn abi Rabi'ah رضي الله عنه
Su kuma wadannan Sahabbai masu Girma Sunyi Karatu Ga babban Sahabinnan masanin Qur'ani UBAYYU IBN KA'AB رضي الله عنه shi kuma ubayyu yayi karatu Ga Annabi Muhammad صلى الله عليه وسلم
Wanna shine Sanadin Riwayar Warsh
Wannan Riwaya ce da warsh ya Riwaito daga Malaminshi Nafi'u kamar Yadda Bayani ya gabata
Haka kuma Wannan Riwaya tanada Dariqoqi Guda biyu Sanannu mafi Shahara
1- Dariqar yusuf Al-Azraq
2- Dariqar Asbahany
Riwayar Warsh tanada Ayoyi 6214 aya Dubu shida da dari biyu da sha hudu
A lissafin Mushafin Madinah na biyu عدد المدني الأخير
Akwai wasu Abubuwa da warsh ya kebanta Dasu sabanin ga riwayarshi kamar
1- Tarqiqin harafin Ra'un ر idan ta cika wasu sharudda
Kamar
خَيرَ
غَيرَ
شَرَرٍ
Da sauransu
(Domin neman sanin wadannan sharudda to a nemi littafan da sukayi magana Akan riwayar Warsh a duba musamman Babi mai magana akan Ra'at wato hukuncin harafin Ra'un ر)
2- Taglizin harafin Lamun ل idan ya cika wasu sharudda
Kamar
مَطْلَع
ظَلَمُوا
صَلَوٰة
Da sauransu
(Domin neman sanin wadannan sharudda to a nemi littafan da sukayi magana Akan riwayar Warsh a duba musamman Babi mai magana akan Lamat wato hukuncin harafin lamun ل)
3 Da kuma Jan Maddar badal
Kamar
ءامنون
إيمان
أوتوا
Da sauransu
Shima wannan Yanada sharudda wadanda ya kamata ace mutun ya sansu
A duba littafan da sukayi magana akan Riwayar Warsh musamman Babin Da yayi magana Akan Maddodi
ABUBUWAN DA YA KAMATA MU SANI GAMEDA USUL NA RIWAYAR WARSH
1- Hukuncin bisimillah
2- Hukuncin mimul-jam'i
3- Hukuncin Maddodi
4- Hukuncin harafin Hamzah أ ء
5- Hukuncin izhari da idgami
6- Taq'lili Da Imalah
7- hukuncin harafin Ra'un ر
8- hukuncin harafin Lamun ل
9- Ya'atul Idafah
10- Ya'atuzzawa'id
1- HUKUNCIN BISIMILLAH
Warsh yanada Fuska 5 a bisimillah dake Zuwa Tsakanin surori
1- قطع الجميع
Shine Ka kare sura Ka tsaya Kayi bisimillah ka tsa sai ka shiga wata sura
Misali
ولم يكن له كفوا أحد، بسم الله الرحمن الرحيم، قل أعوذ برب الفلق
2- وَصلُ الجميع
Shine ka hade karshen sura da bisimillah da kuma farkon surar da take gaba
Misali
ولم يكن له كفوا أحدٌ بِسم الله الرحمن الرحيمِ قُل أعوذ برب الفلق
3- قطع الأول ووصل الثاني بالثالث
Shine Ka kai karshen sura ka tsaya Sai kuma ka hade Bisimillah da farkon surar da take gaba
Misali
ولم يكن له كفوا أحد، بسم الله الرحمن الرحيمِ قُل أعوذ برب الفلق
4- الوصل بلا بسملة
Shine ka sadar da karshen surar da ka gama da surar da take a gaban ta ba tareda kayi bisimillah ba
Misali
ولم يكن له كفوا أحدٌ قُل أعوذ برب الفلق
Sai kuwa Akwai wasu surori guda hudu da suka sabawa Wannan tsarin ana kiransu da suna أربَعُ الزُّهُهر
Sune :-
1- سورة القيامة
2- سورة المطففين
3- سورة البلد
4- سورة الهمزة
A nemi littafin Riwayar Warsh domin neman Karin Bayani
5- السكت بلا بسملة
Shine idan ka gama Sura sai ka dan tsaya kadan ba tareda kayi nunfashi ba sai ka shiga surar da take gaba ba tareda kayi bisimillah ba
Misali
ولم يكن له كفوا أحدْ (س) قُل أعوذ برب الفلق
Sai kuwa Akwai wasu surori guda hudu da suka sabawa Wannan tsarin ana kiransu da suna أربَعُ الزُّهُهر
Sune :-
1- سورة القيامة
2- سورة المطففين
3- سورة البلد
4- سورة الهمزة
A nemi littafin Riwayar Warsh domin neman Karin Bayani
2- HUKUNCIN MIMUL-JAM'I
Mimul-jam'i م mimun ce da take zuwa a Qurani domin nuni akan Jam'i (abunda ya wuce biyu)
Warshu yana karantawa da yin silar mimul-jam'i idan Aka samu Harafin Hamzah ء yazo a gaban ta
Misali
سواء عليهم ءأنذرتهم
وإذا قيل لهم ءامنون
Da sauransu
Amma idan Harafin Hamzah ء baizo ba to Warsh baya yin silar ta
Misali
صراط الذين أنعمت عليهم غير المغضوب عليهم ولا الضالين
Da sauransu
3 HUKUNCIN MADDODI
Warsh yana ja 6 ga maddul wajib da kuma ja'iz
Haka kuma yana fuska biyu A wurin maddul lin المد اللين wacce takeda harafin hamzah ء a cikinta
Misali
شَيء شَيئا هَيئة
Yana ja 4 ko 6 a wannan maddar
Sai dai akwai kalmomin da aka togaci (aka ware) wadanda baayimusu maddar
A nemi Littafin da yayi magana akan riwayar Warsh domin neman karin bayani
Haka ma yanada fuska uku a wurin Maddul badal
Kamar
ءامنون إيماناً. أوتوا
Da sauransu
Yana ja 2 ko 4 ko 6 ga maddul badal
Sai dai akwai kalmomin da aka togaci (aka ware) wadanda baayimusu maddar
A nemi Littafin da yayi magana akan riwayar Warsh domin neman karin bayani
4- HUKUNCIN HARAFIN HAMZAH ء
Akwai Hamzah kala uku da ya kamata ace munyi magana akansu a wannan babin
Sune
1- الهمزتين من كلمة
2- الهمزتين من كلمتين
3-الهمز المُفرد
1- الهمزتين من كلمة
Sune Hamza biyu dake Zuwa a tare a cikin kalma daya
Misali
ءأنذرتهم ءألد ءأمنتم
Da sauransu
2- الهمزتين من كلمتين
Shine a samu Hamza tazo A karshen kalma ta farko sai kalmar da take a gabanta ta fara da harafin Hamza ء
Misali
جَاءَ أُمة
نَشاء أصبناهم
من السماء أو ائتنا
Da sauransu
3- الهَمز المُفرد
Itace Hamzah da take zuwa guda daya a cikin Kalma
Misali
يؤمن يأت يؤتَونَ يأجوج ومأجوج
Da sauransu
Warsh Yana yin Tas'hili a dukkan wadannan nau'uka uku na wadannan Hamzojin
Ha kuma yanayin Ibdali A wasu daga cikinsu
A nemi littafin da yayi magana akan Riwayar Warsh Domin neman karin bayani
5- HUKUNCIN IZHARI DA IDGAMI
Warsh bai sabawa hafsu ba a wurin izharin nunussakina da tan'wini ko lam Al da sauran tajwidi da muka sani
Inda ya sabawa Hafs shine wuraren da zamu kawo
👇👇👇👇
Duk inda aka samu قَد tazo sai harafin ض ko ظ sunzo a gabanta to warsh yana yin Idgamin harafin د a cikin daga daga cikin wadannan haruffa
Misali
قال لقَد ظَّلمك
فَقَد ضَّل سواء السبيل
Da sauransu
Haka kuma idan aka samu Ta'utta'anis (تاء التأنيث) sai aka samu harafin ظ yazo a gaba to nan ma warsh yana yin idgami
Misali
كانت ظَّالمَةً
Da sauransu
Haka kuma yana idgami ln wadannan kalmomin
أَخَذتَّ أَخَذتُّم اتَّخَذتَّ. اتَّخَذتُّم
Da makamantansu
6- TAQLILI DA IMALAH
Mafi yawan Mutane suna yiwa warshu Gurguwar fahimta a wannan babin
Sai kaji mutum yana karatu da Riwayar Warsh amma sai ya rika yin Imalah a wuraren da ya kamata yayi Taq'lili
Warshu bayada IMALAH in ba a wuri daya ba shine ga harafin ه wurin kalmar طــه a farkon suratu طــه
A nan ne kawai mutun zaiyi Imalah idan yana karatu da Riwayar Warsh
Sauran Duk Taq'lili ne ko shi kuwa yanada ka'idoji da sharuda da ya kamata mu nemi littafin da yayi magana akan Wannan Riwayar domin neman karin Bayani
Wasu kuma suna kiran Taq'lili da sunan IMALAH SUGRA wato Karamar Imalah
7- HUKUNCIN HARAFIN RA'UN ر
Warsh yanada wani hukunci da ya kebanta shikadai a wurin Harafin Ra'un
Shine yimata tarqiqi bayan Tarqiqi da sauran Riwayoyi suke yimata
Shine Tarqiqin harafin Ra'un ر idan ta cika wasu sharudda
Kamar
خَيرَ
غَيرَ
شَرَرٍ
Da sauransu
(Domin neman sanin wadannan sharudda to a nemi littafan da sukayi magana Akan riwayar Warsh a duba musamman Babi mai magana akan Ra'at wato hukuncin harafin Ra'un ر)
8- HUKUNCIN HARAFIN LAMUN ل
Warsh yanada wani hukunci da ya kebanta shikadai a wurin Harafin LAMUN ل
Shine yimishi Taglizi bayan Taglizi da sauran Riwayoyi suke yimata
Shine Taglizin harafin Lamun ل idan ya cika wasu sharudda
Kamar
مَطْلَع
ظَلَمُوا
صَلَوٰة
Da sauransu
(Domin neman sanin wadannan sharudda to a nemi littafan da sukayi magana Akan riwayar Warsh a duba musamman Babi mai magana akan Lamat wato hukuncin harafin lamun ل)
9- YA'ATUL IDAFAH (ياءات الإضافة)
YA'ATUL IDAFA
Ita wannan Ya'un Tanada Halaye biyu a wurin Qurra Akwai masu yimata Fat'ha
Kamar
إِنِّــيَ أَعلَم
إِنِّــيَ أُرِيد
دُعَآءِى إلا فرارا
haka kuma akwai masu Yimata Skun
Kamar
إِنِّــيٰٓ أَعلَم
إِنِّــيٰٓ أُرِيد
دُعَآءِىٰٓ إلا فرارا
Shima warsh Yabi Sahun Sauran Riwayoyi a wannan babin
Akwai wuraren da yake yimata fat'ha kuma Sune sukafi yawa
Akwai kuma wuraren da yake yimata skun Sune sukafi karanci
Domin neman Karin bayani a binciki littafan wannan Fannin
10- YA'ATUZ-ZAWA'ID ياءات الزوائد
Ita kuma wannan Itama ya'un ce da Asalinta baarubuce take ba a cikin Qur'ani, kuma Qurra'u sunyi sabani a gareta sunyi sabani kashi uku
1- Akwai masu karanta ta A kowane irin yanayi ( lokacin tsayawa WAQAFI a kanta, ko lokacin wucewa da karatu a kanta) kamar Ibn Kathir
2- Akwai Wadanda basu karantawa da ita A kowane irin yanayi Na karatu ( lokacin tsayawa WAQAFI a kanta, ko lokacin wucewa da karatu a kanta) Kamar Hafsu
3- Akwai wadanda ke Tabbatar da ita a lokacin wucewa da Karatu Kamar warsh, suna cireta wurin WAQAFI
Aduk wurin da warsh yake da YA'ATUZ-ZAWA'ID to yana karanta ta ne Kawai idan zai wuce da karatu a mma idan xai tsaya a kan kalmar da take dauke Da ita To kaitsaye yana cireta
Ya'atuz-zawa'id Tana zuwa ne a cikin wadannan kalmomin da ire-iren su
👇👇👇👇
إلى الداع
واليل إذا يَسر
الجَوَار
الجَواب
يناد المناد
Da sauransu
Domin neman Karin Bayani a Bincika cikin littafan wannan Fannin
Anan zamu tsaya sai a taremu a rubutu na gaba inda zaa jimu da wata Qira'ar ta daban insha Allah
JAN HANKALI
👇👇👇👇
Duk wanda Zaiyi sharing ko Kwafi Na wannan Rubutun nawa To ya yi Sharing Dinshi A yadda Na Rubutashi Kar ya kara komai kuma Kar ya canja komai abar shi yadda nayishi
Duk wanda yakeda Taaliki ko gyara Ko shawara ko Mulahaza akan Wannan Rubutun to ya atuntubeni nizan gyara Da kaina Amma Kar A canja Min rubutu.
Ga lambar da zaa tuntubeni da ita +2348034468543
✍️WANDA YA RUBUTA
Habibu Muhammad Shugaba
+2348034468543
Tuesday
11-11-1442
22-06-2021