Monday, 14 March 2022

RUBUTU NA 9: TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20 | تاريخ القراء العشرة ورواتهم

  رِوايةُ الدُورِي

عَن أبِـي عَمرو البَصري
TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20
تاريخ القراء العشرة ورواتهم
RUBUTU NA: 9️⃣
Rubutawar
✍Habibu Muhammad shugaba
ABUBUWAN DA KE KARKASHIN WANNAN RUBUTUN
👇👇👇👇👇
1- WANENE AL-IMAM AL-DURY
2- MALAMAN AL-IMAM AL-DURY
3- DALIBAN AL-IMAM AL-DURY
4- BAYANI AKAN USUL NA RIWAYAR AL-IMAM AL-DURY
1-WANENE AL-IMAM AL-DURY
SUNANSHI:- hafs bn umar ibn Abdul-aziz ibn suhban ibn Adiy ibn Suhban.
ALKUNYARSHI:- Abu umar
LAKABINSHI:- AL-DURY, nisba ce zuwa ga Garin da aka haifeshi mai suna DUR.
Dur, sunan gari ne da ke Gabas ga garin Bagdad
An haifeshi a Garin Al-dur a shekara ta 150 bayan Hijrah a zamanin khalifancin Al-mansur ( khalifa na biyu Daga cikin Khalifofin Banul-Abbas 136AH-158A.H)
Ya Rasu a shekara ta 246 Bayan Hijrah a zamanin Khalifancin Al-mutawakkil ( Khalifa na Goma daga cikin Halifofin Banul-Abbas 232-247)
رحمه الله رحمة واسعة
Al-imam Al-dury masanin Qur'ani ne da Qira'o'in shi haka kuma Masanin Nahawu ne da sauran ilmukan Addini
Shine farkon wanda ya fara yin Rubutu akan Ilimin Qira'o'i
Shine Shugaban Makaranta Qur'ani a zamaninshi musamman mutanen Iraqi
Mutane sun kasance suna Zuwa daga sassa Daban-daban na duniya domin suyi karatu a wurinshi
Ya karanci Qira'o'i Daban-daban na Al-Qur'ani mai girma
=Ya karanci Qira'ar Abu Amr Al-basry a wurin Yahya ibn Al-mubarak Alyazidiyyi
=Ya karanci Qira'ar Hamzah a wurin Sulaim
=Ya karanci Qira'ar Kisa'i a wurin Kisa'i da kanshi
=Ya karanci Qira'ar Abu ja'afar a wurin Yaakub ibn Ja'afar daga Ibn jammaz daga Abu Ja'afar
=Ya karanci Qira'ar Nafi'u daga Isma'il ibn Ja'afar
Da sauransu
2- MALAMAN AL-IMAM AL-DURY
Daga cikin Maluman shi Akwai
1- Isma'il ibn jaafar
2- Yaakub ibn jaafar
3- sulaim ibn isah
4- muhd ibn saadan
5- Aliyu Al-kisa'i
6- Hamzah ibn Alkasim
7- Yahayal-yazidiyyi
Al-imamul-ahwaziy yace:- Al-imam Al-dury ya Shiga Duniya wurin neman ilimin Qira'o'i, kuma ya samu ilimin, ya san ilimin Qira'o'i Mutawatirai, sahihai, Shawadh, da kuma munkarai.
3- DALIBAN AL-IMAM AL-DURY
Al-imam Al-dury yanada Dalibai masu dinbin yawa
Ga kadan daga Cikin su
1- Ahmad ibn Harb
2- Ahmad ibn Farh
3- Abu ja'afar almufassir
4- Ahmad ibn yazid Alhulwaniy
5- Ahmad ibn Mas'ud Al-siraj
6- Ishaq ibn Ibrahim Al-askariy
7- Isma'il ibn Ahmad
8- Isma'il ibn yunus
9- Sa'id ibn Abdurrahim
10- Alhassan ibn Al-haddad
Da sauransu
4-BAYANI AKAN USUL NA RIWAYAR AL-IMAM AL-DURY
Riwayar Dury daga Abu amr al-basry daya ce daga cikin Riwayoyinshi biyu da yayi ga Abu Amr al-basry da kuma Kisa'i Saboda Haka Yanada Kyau Mu Sani cewa Shi din dai ne da yayi Riwaya ga Abu Amr al-basry yayi Riwaya ga Kisa'i saboda haka Yanada RAMZI biyu a cikin Littafin Shadibiyyah
1- Harafin ط shi ke nuni akan Riwayar da yayi daga Abu amr al-basry
2- Harafin ت dake nuni Akan Riwayar da Yayi daga Kisa'i
Wani Mai Wake Yana cewa
وَإِ قِيلَ لِلدوريِّ حَرفَانِ لِمْ لَهُ
فَقل عَن عَلِيِِّ تَا وَطَا عَن فَتَى العَلَا
Maana Idan Akace meyasa Dury yakeda Ramzi Biyu? Kace Harafin ت yana nuni ne akan Riwayar da yayi Daga Aliyu ( Kisa'i) Harafin ط kuma yana nuni akan Riwayar shi Daga Fatal-Ala ( Abu Amr al-basry)
والله أعلم
Haka Kuma Riwayar Dury Itace Ake Gabatarwa Akan Riwayar susi A wurin Jerantawa
GA WANI BAYANI MAI MUHIMMANCI DA YA KAMATA MU SANI
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇
mu sani cewa Duriy da Susiy Basuyi Karatu Kaitsaye (Baki da baki) Ga Abu Amr ba, sunyi karatu ne ga Yahya ibn Al-mubarak Al-yazidiy ( يَحْيَى اليَزِيدي) wanda Imamus-shadibiy yake cewa Game da shi :
= أَفَاضَ عَلى يَحْيَى اليَزِيديِّ سَيْبَهُ
فَأَصْبَحَ بِالعَذْبِ الفُرَاتِ مُعَلَّلا
= أبُو عُمَرَ الدُّوري وَصَالِحُهمْ أبو
شُعَيبٍ هُو السُّوسِيُّ عَنهُ تَقبَّلا
Fassara
= Abu Amr Al-basry ya Zubawa yahyal-yazidiyyi Baiwarshi ( iliminshi) yahya ya kasance kosasshe saboda ingantaccen ilimin da ya kwankwada daga Abu Amr.
= Abu umar Ad-dury da kuma salihu mai Alkunya Abu Shu'ai wanda shine Ake kira Susi, Sun karbi Qira'ar Abu Amr a gareshi (يَحْيَى اليَزِيديِّ).
Ma'ana dai Akwai wasida a tsakanin su da Abu Amr
Nayi bayani a rubutu na na farko cewa
Wadanda ake Jinginawa riwayoyi (Masu Riwaya) Sun kasu gida uku
1- akwai wadanda sukayi karatu baki da baki ga QARI'AI da ake jinginawa riwayarsu zuwa garesu kamar
- Qalun da warsh sunyi karatu baki da baki ga Nafi'u
2- Akwai wadanda A tsakaninsu da QARI'AN akwai wasidar Mutun Daya kamar
- Dury da susi Sunyi karatu ga Yahyal-Yazidiyyi shi kuma yahya yayi karatu ga Abu Amr Al-basry
-Kamar Khalaf da khallad Sunyi karatu ga Sulaim shi kuma sulaim Yayi Karatu Ga Hamzah
3- Akwai wadanda akwai fiye da mutun daya a tsakaninsu da QARI'IN DA sukayi riwaya a gareshi kamar
- Bazzi da Qumbul basuyi karatu kai tsaye ga ibn kathir ba Akwai fiye da mutun daya a tsakanin su
Abun da yasa hakan ta faru shine
A lokacin da wannan ilimin na riwayoyi yayi yawa ya fadada riwayoyin sunyi yawa Kasancewar kowane Qari'i yanada dalibai masu dinbin yawa kuma kowane daga cikin su yana jingina riwayar shi zuwaga wannan Qari'in
Sai akayi niyyar Takaita Riwayoyin Akace kowane QARI'I zaa fitar da mutun biyu daga cikin Rawiyanshi (Dalibanshi) Wadanda sukafi kwarewa da kuma tsoron Allah Da tsantseni domin a jingina riwayar shi zuwa garesu
Sai a bincika Idan an samu wanda ya cika sharudan daga cikin Daliban QARI'IN, haka kuwa akayi Zabin Ya fada Ga Duriy da Susi sai aka aka cigaba da jingina Qira'ar Abu Amr Al-basry zuwa garesu, Riwayar su kuma ake jinginata kai tsaye zuwa gareshi (Abu Amr Al-basry) Sabanin asalin Malaminsu ( yahyal-yazidiyyi)
Wannan shine Ma'anar Fadar Shadibiyy
تَخَيرَهم نُقَّادُهُم كلَّ بَارِعٍ
وَلَيسَ عَلى قُرءَانِه مُتَأَكِّلا
Adadin Ayoyin Qur'ani na wannan Riwayar 6214
An sanya adadin Al-madany Al-auwal ( wato tsarin Kirga Ayoyin Al-madany na farko) dama tsarin Qirga Ayoyin Qur'ani akwai
المَدَني الأول
المدني الثاني
Akwai na makkah da sham da kufa da Basrah,
جَعلتُ المَدينِي أَولاً ثم ءاخِرا
وَمَكٍ إلى شَامِِ وكوفٍ إلى بَصْري
Haka Shadibiyy yace a cikin littafinshi ناظمة الزهر في عد آي السور
عد المدني الأول
Shine kafatanin Mutanen basrah ke aiki dashi a mushaf na Abu Amr da ya'akub
Adadin ayoyin su sune Dubu shida da dari biyu da sha hudu 6214
RAMZIN QIRA'AR ABU AMR AL-BASRY
Al-imam As-shadibiy ya yiwa Qira'ar Abu Amr Ramzi ( wato alamar da zai rika yin nuni akan Qira'ar Abu Amr da ita), Ramzin shine
HUDDI (حُطِّي)
wato idan akaga Ramzi na harafin ح a cikin Shadibiyyah to yana nuni ne akan Abu Amr Al-basry
Idan akaga Ramzi na harafin ط yana nufin Duri an Abi Amr
Idan akaga Ramzi na harafin ي to yana nufin Susi
Duk da cewa zai iya kiran kowane daga cikin su da sunanshi ko lakabinshi kai tsaye idan wazanin wakar ya bayar da damar yin haka.
Muna yin rubutun ne a takaice da sai mu bayar da misalin ko wanne daga cikin su, amma idan an koma Shadibiyyah zaa samu misallansu da yawa.
GA ABUBUWAN DA ZAMUYI BAYANINSU NA USUL DIN WANNAN RIWAYAR
1- BISIMILLAH DAKE ZUWA TSAKANIN SURORI BIYU ما جاء بين السورتين
2- HA'UL KINAYAH (هَاء الضمير)
3- MADDODI المدود
4- HUKUNCE-HUKUNCEN HAMZA
5- NAQLU DA SAKT النقل والسكت
6- IDGAMI الإدغام
7- IMALAH الإمالة والتقليل
8- WAQAFI AKAN WASU HARUFFA DA SABANIN YADDA AKA RUBUTASU
9- YA'ATUL IDAFAH
10- YA'ATUL-ZAWA'ID
1- BISIMILLAH DAKE ZUWA TSAKANIN SURORI BIYU ما جاء بين السورتين
Al-imam Al-dury yanada Fuska 5 a wurin bisimillah dake Zuwa Tsakanin surori
1- قطع الجميع
Shine Ka kare sura Ka tsaya Kayi bisimillah ka tsa sai ka shiga wata sura
Misali
ولم يكن له كفوا أحد، بسم الله الرحمن الرحيم، قل أعوذ برب الفلق
2- وَصلُ الجميع
Shine ka hade karshen sura da bisimillah da kuma farkon surar da take gaba
Misali
ولم يكن له كفوا أحدٌ بِسم الله الرحمن الرحيمِ قُل أعوذ برب الفلق
3- قطع الأول ووصل الثاني بالثالث
Shine Ka kai karshen sura ka tsaya Sai kuma ka hade Bisimillah da farkon surar da take gaba
Misali
ولم يكن له كفوا أحد، بسم الله الرحمن الرحيمِ قُل أعوذ برب الفلق
4- الوصل بلا بسملة
Shine ka sadar da karshen surar da ka gama da surar da take a gaban ta ba tareda kayi bisimillah ba
Misali
ولم يكن له كفوا أحدٌ قُل أعوذ برب الفلق
Sai kuwa Akwai wasu surori guda hudu da suka sabawa Wannan tsarin ana kiransu da suna أربَعُ الزُّهُهر
Sune :-
1- سورة القيامة
2- سورة المطففين
3- سورة البلد
4- سورة الهمزة
A nemi littafan Riwayoyi domin neman Karin Bayani
5- السكت بلا بسملة
Shine idan ka gama Sura sai ka dan tsaya kadan ba tareda kayi nunfashi ba sai ka shiga surar da take gaba ba tareda kayi bisimillah ba
Misali
ولم يكن له كفوا أحدْ (س) قُل أعوذ برب الفلق
Sai kuwa Akwai wasu surori guda hudu da suka sabawa Wannan tsarin ana kiransu da suna أربَعُ الزُّهُهر
Sune :-
1- سورة القيامة
2- سورة المطففين
3- سورة البلد
4- سورة الهمزة
A nemi littafan Riwayoyi domin neman Karin Bayani
2- HA'UL-KINAYAH هَاءُ الكِنَايَة KO KUMA MUCE هاء الضمير
Ha'ul-kinayah Ha'un ce Da ke nuni akan wani abu daya namiji (المُذَكَّر) Wanda bayanan الغَائِب Kamar عليه da فيه da sauran su
Akwai sabanin riwayoyi a wurare da dama a wurin wannan Ha'un din kamar haka
1- wasu suna Daure ta a wasu wuraren kamar. يُؤَدِّهْ إِلَيك
2- wasu kuma Wasu suna Yimata Wasali ba tare da anja mata Madda Ba (Sila) kamar. يُؤَدِّهِ إِلَيك
3- wasu kuma Suna Yimata Wasali tareda Silar ta wato jan Madda Gareta kamar يُؤَدِّهِ> إِلَيك
A nemi littafan Riwayoyi domin sanin matsayin kowace riwaya a wannan Babin
Al-imam Al-dury yana Karanta wadannan Ha'un din tareda daureta gasu kamar haka
يُؤَدِّهْ إِلَيك
نُؤْتِهْ منها.
نُوَلِّهْ ما تولى.
نُصْلِهْ جهنم.
وَيَتَّقِّهْ فأولئك هم الفائزون
Yana Cire madda A wurin
فيهِ مُهَانًا
Sabanin yadda hafs da ibn kathir ke karantawa
Yana mayar da Dwammar Ha'un Ta dawo Kas'ra a wurin wadannan kalmomin
وَمَــــا أَنسَـــٰـــنِيهِ إلا الشيطـن
عَلَيهِ اللهَ
Sabanin yadda Hafs ke karantawa
Haka ma yana kara Harafin Hamzah ء Tareda yin Dwammar Ha'un هُ saidai ba tareda yin sila gareta
👇👇👇👇👇
أَرْجِئْهُ وَأَخَاهُ
Haka kuma yanada Fuska Biyu a kalmar
يَرْضَهُ لكم
Gasu kamar haka
1- يَرْضَهْ لكم daure Ha'un
2- يَرْضَهُ,لكم Dwammar Ha'un tareda Sila
3- MADDODI المدود
Maddah Itace Jan Sauti Domin zuwan Daya daga Cikin Haruffan Madda Guda Uku sune. ا da و da ي
Alif Daurarra Idan Harafin da ke gabaninta kamar قَالَ
Wawun Daurarra idan Harafin da ke Gabaninta yanada Dwwmma ُ kamar نُوح
Ya'un Daurarra idan Harafin da ke Gabaninta yazo da Kas'ra ِ kamar قِيلَ
Al-imam Al-dury yana Ja 4 a wurin Maddul-wajib
المَد الواجب المتصل
Haka kuma yanada Fuska Biyu A wurin maddul-ja'iz
المُنفَصِل
1- ja biyu 2
2- ja hudu 4
4 HUKUNCE-HUKUNCEN HAMZA
Wannan babin Kuma munada babi uku 3 da zamuyi bayanin Hamzah dake a cikin wadannan babukan
1- الهمزتين من كلمة
2- الهمزتين من كلمتين
3-الهمز المُفرد
1- الهمزتين من كلمة
Sune Hamza biyu أأ dake Zuwa tare a cikin kalma daya
Misali
ءأنذرتهم ءألد ءأمنتم
Da sauransu
Al-imam Al-dury yana yin Tas'hiln Hamzah ta biyu Tareda yin Id'khali (Abunda Ake cewa Id'khali shine Ayi madda Tsakanin Hamza guda biyu) idan aka samu Hamzah biyu sunzo a cikin kalma daya kamar haka
ءَ ٰاْنذرتهم
ءَ ٰاْلد
ءَ ٰاْمنتم
Saidai kuma Akwai Hamzar da Tas'hili kawa yake yi banda Id'khali
Haka kuma yana Kara harafin Hamza A wadannan Kalmomin Kuma yayi Tas'hilin Hamzah ta biyu
👇
أَينَّ لَنَا لأَجرا Cikin Suratul A'arof
أينَّكم لتأتون الرجال A'arof da Ankabut kissar Annabi Lud
Yana Tashilin Hamzah a wannan kalmar da Ta maimaitu sau uku
ءَاْ ٰمَنتُم لَه قبل أن
ءَاْ ٰمَنتُم به قبل أن
Haka kuma yana yin Tas'hilin
ءاْ ٰلِهَتُنَا خير أم هو
Haka kuma yana sanya Wa wannan Kalmar Madda
مَاجِئْتُم بِهِ ءَآلسِّحْر
Maimakon
مَاجِئْتُم بِهِ السِّحْر
Yadda Hafs da sauran riwayoyi ke karantawa
A nemi Littafan Qira'o'i domin neman Karain Bayani
2- الهمزتين من كلمتين
Sune a samu Hamza tazo A karshen kalma ta farko جآء sai kalmar dake biye da ita ta fara d a harafin Hamzah 👉أمة
(جَاءَ أُمة)
Misali
جَاءَ أُمة
نَشاء أصبناهم
من السماء أو ائتنا
Da sauransu
Al-imam Al-dury Yana Cire Hamza ta Biyu ko ta Farko a duk inda Aka samu Hamza Biyu sunzo cikin kalmomi biyu Kuma Sukayi ittifaqi a wurin wasali MISALI
جَآءَ أَجَلُها
هؤلاءِ إِن كنتم صدقين
أولياءُ أُولئك
Idan muka dubi wadannan misalai uku zamuga cewa Duka Hamzar da ke cikin kowace kalma wasalinsu daya
To Dury yana cire Hamza daya Daga cikin wadannan Hamzojin ya bar daya sai ya karanta
جَا أَجَلُها
هؤلا إِن كنتم صدقين
أوليا أُولئك
Saidai malamai sunyi magana Akan Maddar dake wurin sukace
Idan Hamza Ta farko akan cire kamar جَا أَجَلُها to yanada Ja 2 ko ja 4 wurin madda Domin ta dawo المد الجائز
Idan kuma Hamza ta biyu aka Cire kamar جَآءَجَلُها to Yanada Ja 4 kawai Saboda Tana nan akan Maddul-wajib
A koma littafai domin neman karin bayanin
Amma idan wasullan wadannan Hamzojin sun banbanta misali ta farko tanada dwamma ءُ ta biyu tanada fataha ءَ Misali
نَشَآءُ أَصَبنَــٰــهم
Ko kuma a samu ta farko tanada kasra ءِ ta biyu tanada fataha ءَ Misali
مِنَ السََّمَآءِ ءَاية
Da dai sauransu
To idan aka samu sun sa6a a wurin wasali To Dury yana Yin Tas'hilin Hamza ta biyu kamar haka
👇👇
نَشَآءُ اْصَبنَــٰــهم
مِنَ السََّمَآءِ °َاية
Da sauransu
3- الهَمز المُفرد
Itace Hamzah da take zuwa guda daya a cikin Kalma daya
Misali
يؤمن جِئت هِئتَ. شِئتَ يأت يؤتَونَ يأجوج ومأجوج
Da sauransu
Wurare da yawa Hafs yana Tareda Dury a wannan Babin
Saidai sunyi sabani kala Biyu
1- akwa wurinda Hafs ke saka Hamza Shi kuma Dury ya Cire kamar
ياجوج وماجوج
يُضَـــٰـــهُونَ قَول الذين كفروا
الَّــــــٰٓــــــيْ a surar Ahzab da Mujadalah da Dalaq
هَـــــٰـــــاْنتُم Duk inda Tazo Yana yin Tashilin Hamzar yamada Fuska Biyu a wurin Madda Ja2 ko ja 4
2- Akwai wurin da hafs Ke Cire Hamza Shi kuma Dury ya Saka Hamzar kamar
بَادِئَ الرَّأْيِ. Suratu Hud
وءاخَرُون مُرْجَئُونَ لِأمر الله
تُرْجِئُ مَن تَشَآء منهن
لَا يَأْلِتْكُم من أعمالكم شيئا suratul Hujurat
Idan muka Duba Dakyau zamuga Karara Sun Saba A wadannan Kalmomin da muka kawo
والله أعلم
A nemi littafin da yayi magana akan wannan Riwayar Domin neman karin bayani
5- NAQLU DA SAKT النقل والسكت
Abunda ake cewa NAQLU shine Cirato wani abu Zuwa wani abu, Anfi amfani da wannan isdilahin Ga Hamza a wurin maluman Qira'o'i kamar ace
نقل حركة الهمزة إلى الساكن قبلها
Wato cirato Wasalin Hamza a dorashi kan Harafin da ke Gabaninshi kamar ace
قَدَ افْلَحَ
مَنُ اوتِـيَ
Da sauransu
Warshu shine mai wannan Babin
To Al-imam Al-dury yana NAQLU a wuri daya A cikin Qurani mai Girma suratul-Najm
عَادًا الُّاولـى
Idan muka duba zamuga cewa an shafe Hamza
SAKTAH:- Tana nufin Tsayawa dan lokaci kadan a yayin Karatu ba tareda Shedawa ba sannan a wuce kamar كَلَّا بَل رَان sananne a Riwayar Hafs
To Al-imam Al-dury bayada Saktah Ko daya don Haka duk wuraren nan Da hafs keyinta wuri 4 shi bayayi, Ga wuraren kamar Haka
1- ولم يجعَل له عِوَجا(١) قيما لينذر بأسا شديدا
2- من بَعَثَنَا من مرقَدِنا هذا ما وَعَدَ الرحمن
3- وقِيلَ مَن رَاق
4- كلا بل ران على قلوبهم
Baya yin Sak'tar wadannan wuraren
6- AL-IDGAM الإدغام
Shine Shigar da Wani Abu a cikin wani abu
Akwai wasu Haruffa da ke Shiga cikin wasu kuma Riwayoyi sunyi sabani a garesu wato wasu suna Izhari wasu kuma Suna Idgami
Akwai
(إِذْ) ت ز ص د س ج harafi 6
(قَدْ) harafi 8 س ذ ض ظ ز ج ص ش
(تَاء التأنيث) harafi 6 س ث ص ز ظ ج
(هَل) ( بَل) harafi 8 ت ث ظ ز س ن ط ض
Akwai haruffan Da ke shiga cikin wadannan Haruffan musali
إِذْ
Haruffa 6 ke shiga cikin إِذْ sune
ت ز ص د س ج
Kamar
إِذ تَّمشِي أُختُكَ
إِذ سَّمِعْتُمُوهُ
Da sauransu
Al-imam Al-dury yana Yin idgamin wadannan Haruffan gaba daya Saidai wurin هَل da بَل yana Idgamin
هَل تَّرى من فطور
هَل تَّرى لهم من باقية
Kawai
Haka kuma Yana Idgamin wadannan Kalmomin da zan jero
Idgamin Ba'un Mai Jazama (Dauri) Misali
يَغْلِب فَّسَوفَ
Da kuma
عُذتُّ بربـي
فَنَبَذتُّهَاَ
Da kuma
أَخَذتَّ أَخَذتُّم
اتَّخَذتَّ. اتَّخَذتُّم
لَبِثتَّ. لَبِثتُّم
أُورِثتُّمُوهَا بما كنتم
كهيعصٓ ذِّكرُ idan zaa wuce
مَن يُرِدثَّوَابَ
وَيُعَذَِب مَّن يشاء bakarah
Yanada Fuska Biyu ga
وَاصْبِرلِّحكم ربك
Da ire-iren shi
7- IMALAH الإمالة والتقليل
Nan Kuma Zamuyi bayani a takaice Matsayin Al-imam Al-dury akan Wannan Babin
Riwayoyi sun kasu Gida Uku gameda abunda ya shafi Wannan Babin
1- Akwai wadanda Basuda Imala Ko Taq'lili ko daya Kamar Qira'ar Ibn Kathir da Abu Ja'afar
2- Akwai wadanda Imalah Daya Kawai Garesu Kamar, QALOON, warshu, Hafs,
Saidai kuma Warsh Yanada Taq'lili da yawa
3- Akwai masu Imaloli da Yawa kamar, Hamza da Kisa'i, Abu Amr da sauransu
Al-imam Al-dury Yana Daya Daga Cikin Riwayoyi masu imaloli da yawa Saboda haka saidai mu danyi karin Haske Bazamu samu damar Kawo imalolinshi gaba daya ba
Ga Tsarinshi
1- Akwai kalmomin da yakeyin Imala a garesu kamar
أسرى بُشرى
الدارِ النارِ
قَرَارِِ الأبرَارِ
كافِرين الكفرين mai ya'un ي ba mai wawun ba
التورىة
الٓـــــــــر. الٓــــــمٓـــر
الناسِ mai kasra
Haka kuma yana Imala Ga Harafin أ na Kalmar رَأَى idan an Samu Harafi mai Wasali yazo Gaba kamar رَأَى كَوكبًا Yana yin imala ne ga harafin Hamzah yayi Fataha ga Harafin رَ
Amma idan Harafi mai Dauri ne to bayayi kama
رَأَى القَمر رَأَى الشمسَ
Haka Kuma yana yin imala ga kalma أَعْمَى ta farko wurin fadar Allah.
ومن كان في هذه أَعْمَى فهو في الآخرة أَعْمَى
Yayi Fat'ha ga أَعْمَى ta biyu
Haka kuma yana yin imala ga harafin هَ farkon Suratu Maryam
كهيعص
2- Akwai kalmomin da yakeda Fuskoki biyu Ko fat'ha Ko imala
تَتْرََا
Wurin fadar Allah
ثم أرسلنا رُسْلَنا تَتْرََا
Da kuma
يَـــٰـــبُشرَ ٰيَ هَذَا غُــلـٰم
Ko Imalah ko Taq'lili ko fat'ha
3- akwai wuraren da yakeyin Taq'lili kamar
Idan an samu Kalma Tazo bisa Wazanin فَعْلى kamar
سَلْوى. .مَرضى.
Ko wazanin فُعْلَى kamar
طُوبَـى مُوسَى
Ko wazanin فِعْلَى kamar
عِيسَى. إِحْدَى
Da dai makamantansu
Haka kuma Akwai wasu surori goma sha daya 11 da yakeyin Taq'lilin Karshen Ayoyin su رءوس الآي idan wurin ya cika Sharadin Taq'lilin ko yayi Imalah idan wurin ya cika Sharadin Imala
Ga surorin kamar haka
طه النجم. المعارج القيامة. النازعات. عبس. الأعلى. الشمس. اليل الضحى. العلق.
Haka Kuma Yana yin Taq'lilin wadanda
يَـــٰـويلتى
يَـــٰحسرتـى
يَأسَـفـَى
أَنَّـى
A nemi littafan Riwayoyi domin Karin Bayani
8- WAQAFI AKAN WASU HARUFFA
Hukunce-hukuncen tsayawa akan Ha'utta'anith wacce aka rubuta ta a harafin ت (budaddar ت)
Idan muna Bibiyar Qurani zamuga wasu wurare ana rubuta ت budadda a wurin da ya kamata ace an Rubuta ة rufafa Misali
قرت عين لي ولك
وَجَنَّتُ نَعيم
فطرتَ الله
إلا سُنَّتَ الأولين
لسنتِ الله
ومعصيت الرسول
بَقِيَّت الله
كَلِمَتُ رَبك
أولئك يَرجُونَ رَحمَتَ الله
To wannan Babin Shi zai yimuna bayanin Matsayin AL-DURY akan yin Waqafi akan wannan ت
A duk wurin da aka ga irin wannan تTo mu sani Cewa Dury yana yin waqafi tare da Daure Ha'un هْ ne Misali
قرت عين لي ولك. 👈 قُرَّهْ. ( idan zaa tsaya )
وَجَنَّتُ نَعيم. 👈 وَجَنَّهْ ( idan zaa tsaya )
فطرتَ الله. 👈 فطرهْ ( idan zaa tsaya )
إلا سُنَّتَ الأولين. . 👈 سُنَّهْ ( idan zaa tsaya )
ومعصيت الرسول 👈 معصيَهْ. ( idan zaa tsaya )
بَقِيَّت الله. 👈 بَقِيَّهْ. ( idan zaa tsaya )
كَلِمَتُ رَبك 👈 كَلِمَهْ ( idan zaa tsaya )
أولئك يَرجُونَ رَحمَتَ الله. 👈رَحمَهْ ( idan zaa tsaya )
Da dai sauransu
Sai dai a wadannan kalmomi da zan Kawo yana Tsayawa akan تْ ne ba akan هْ ba
👇👇
أفرأيتم اللَّتَ وَالعُزى 👈اللَّتْ( idan zaa tsaya )
مَرضاتِ الله. 👈مَرضاتْ( idan zaa tsaya )
ذَاتَ بَهْجَةٍ 👈ذَاتْ( idan zaa tsaya )
ولاتَ حِينَ مَنَاص. 👈ولاتْ( idan zaa tsaya )
Ya na daure تْ ne a wurin tsayawa akan wadannan kalmomin dama wasunsu da bazamu samu damar kawosu gaba dayaba
والله أعلم
Haka kuma yana waqafi akan harafin Ya'un ي idan Tsayawa ta kama a kan wannan Kalma
كَأَي
Wurin kalma
وكأين da فكأين
Da sauransu a duk inda sukazo
Hakama yana tsayawa akan harafin Alif ا kalam
أَيُّهَ
Guda uku da sukazo Suratul Nur da Zukhruf da Rahman
وتوبوا إلى الله جميعا أَيُّهَ
وقالوا يأَيُّهَ الساحر
سنفرغ لكم أَيُّهَ
Sai ya tsaya a kansu
أَيُّهَا
Da alif na madda
Haka kuma yana tsayawa akan harafin ك idan tsayawa ta kama a kalamr
وَيكَأن الله da وَيكَأنه لا يفلح
Sai ya tsaya
وَيْكْ
والله أعلم
9-YA'ATUL IDAFAH الياءات الإضافة
Ya'ul Idafah itace ya'un Ce Da mai magana keyin anfani da ita domin Jingina wani abu zuwa gareshi
Wannan Ya'un Ta kasu Kashi-kashi
Kamar haka:-
= Akwai wace harafin Hamzah أإ mai fataha ko kasra ko Dwamma yake zuwa a gabanta
إِنِّــيٰٓ أَعلَم
إِنِّــيٰٓ أُرِيد
دُعَآءِىٰٓ إلا فرارا
= Akwai kuma wacce lamu-Al ( لام ال. التعريف ) ke zuwa a gabanta kamar haka
- لا ينال عَهدِى الظلمين
- عبادى الصلحون
- إنما حرم ربـى الفواحش
Da dai sauransu
= Akwai kuma wacce Hamzatu-waslin (الهَمزَةُ الوَصل) ke zuwa Gabanta kamar
- إنـى اْصطفَيتُك على الناس
- إن قومى اتخذوا
- يأتـى من بعدى اْسمه أحمد
= Akwai kuma wacce Haruffa ke zuwa a gabanta ba Hamzah أ ko Lamu-Al ba Misali
- أين شركآءِى قالوا
- من وراءِى وكانت امرأتي عاقرا
- لكم دينكم ولى دين
- إن أرضِى واسعة
Da sauransu
= A duk Wadannan Sassa Na Ya'atul Idafah akwai wuraren da Dury keyimata Fat'ha Akwai kuma Wuraren da yakeyin Skun (Dauri) Wannan Rubutun Bazai Isa mu Bayyana komai Da komai Ba
Domin neman Bayani A nemi Littafan Da sukayi Bayani Akan Wannan Riwayar Domin neman Karin Bayani
GA WANI MUHIMMIN RUBUTU DA YA SHAFI YA'ATUL IDAFA
👇👇👇👇
Akwai Ya'atul Idafah 212 Dari biyu da sha biyu A cikin Qurani mai Girma
= Wadanda harafin Hamzah أَ mai fat'ha yazo a gabanta 99 ne
= Wadanda harafin Hamzah إِ mai kasra 52 ne
= Wadanda harafin Hamzah أُ mai Dwamma 10 ne
= Wadanda Lam-Al لام التعريف tazo a gabanta 14 ne
= Wadanda Hamzatul-wasli tazo gabansu 7 ne
= Wadanda wasu haruffa na daban sukazo gabansu 30 ne
Wannan shine Takaitaccen jawabi gameda Wannan babin
10- Ya'atuzzawa'id الياءات الزوائد
Ita kuma wannan Itama ya'un ce da Asalinta ba arubuce take ba a cikin Qur'ani, Anyi Ilhakinta ne a cikin Mushafi
Qurra'u sunyi sabani a wurin karanta ta Da kuma Waqafi akanta, sun kasu kashi uku
1- Akwai masu karanta ta A kowane irin yanayi ( lokacin tsayawa (WAQAFI) a kanta, ko lokacin wucewa da karatu a kanta) kamar Ibn Kathir
2- Akwai Wadanda basu karantawa da ita A kowane irin yanayi Na karatu ( lokacin tsayawa (WAQAFI) a kanta, ko lokacin wucewa da karatu a kanta) Kamar Hafsu
3- Akwai wadanda ke Tabbatar da ita a lokacin wucewa da Karatu, suna cireta wurin WAQAFI Kamar warsh Da Al-imam Al-dury
Al-imam Al-dury yana Tabbatar da wannan Ya'un ne kawai A lokacin sadar da karatu
Akwai wuraren da yake saka Ya'un din haka kuma Akwai inda baya sakawa
Sai a nemi littafai domin akarin bayani
Ya'atuz-zawa'id Tana zuwa ne a cikin wadannan kalmomin da ire-iren su
👇👇👇👇
إلى الداع
إذا دَعَان
واليل إذا يَسر
الجَوَار
الجَواب
يناد المناد
Da sauransu
Domin neman Karin Bayani a Bincika cikin littafan da sukayi magana akan Wannan Riwayar.
Anan zamu tsaya sai a taremu a rubutu na gaba inda zaa jimu da wata Riwayar ta daban insha Allah
JAN HANKALI
👇👇👇👇
Duk wanda Zaiyi sharing ko Kwafi Na wannan Rubutun nawa To ya yi Sharing Dinshi A yadda Na Rubutashi Kar ya kara komai kuma Kar ya canja komai abar shi yadda nayishi
Duk wanda yakeda Taaliki ko gyara Ko shawara ko Mulahaza akan Wannan Rubutun to ya atuntubeni nizan gyara Da kaina Amma Kar A canja Min rubutu.
Ga lambar da zaa tuntubeni da ita +2348034468543
✍️WANDA YA RUBUTA
Habibu Muhammad Shugaba
+2348034468543
Sunday
27-01-1443
05-09-2021

RUBUTU NA 8: TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20 | تاريخ القراء العشرة ورواتهم

 قِرَاءَةُ الإِمَام

أبِـي عَمرو ابن العلاء البَصري
TARIHIN QARI'AI GOMA 10 DA RIWAYOYINSU 20
تاريخ القراء العشرة ورواتهم
RUBUTU NA: 8️⃣
Rubutawar
✍Habibu Muhammad shugaba
ABUBUWAN DA KE KARKASHIN WANNAN RUBUTUN
👇👇👇👇👇
ABUBUWA 5 DA WANNAN RUBUTUN YA KUNSA
1- WANENE AL-IMAM ABU AMR AMR AL-BASRY
2- SUWAYE MALAMAN AL-IMAM ABU AMR AMR AL-BASRY
3- MAGANAR MALAMAI AKAN AL-IMAM ABU AMR AL-BASRY
4- SUWAYE DALIBAN AL-IMAM ABU AMR AMR AL-BASRY
5- BAYANI AKAN QIRA'AR AL-IMAM ABU AMR AL-BASRY
1- WANENE AL-IMAM ABU AMR AMR AL-BASRY
Anyi Sabani akan Asalin sunan Abu amr al-basry
Wasu sukace Al-kunyarshi shine sunanshi(أبو عمرو), Wasu kuma sukace sunanshi Zabban, wasu suka fadi sunaye sabanin wadannan.
Wanda akafi Rinjayarwa shine ZABBAN
Sunanshi Zabban ibnil-Ala'i ibn ammar ibn Al-aryan ibn Abdullahi ibn Al-hussain ibn Al-haris ibn Jalhamah ibn Hajar ibn khuza'iy ibn Mazin ibn malik ibn Umar ibn tamim ibn murr ibn add ibn dabikhah ibn ilyas ibn mudar ibn ma'ad ibn Adnan.
Abu Amr Attaimy Al-maziniy Al-basry, Daya ne daga cikin القُرَّاء السبعة ( Wato QARI'AI 7 na Qur'ani)
Al-hafiz Abul-ala'i Al-hamzaniy yace: Wannan itace ingantacciyar nasabar Abu Amr Al-basry wacce masana Nasaba suka Tabbatar.
Abh Amr Al-basry ya kasance mafi sanin mutane Al-Qur'ani Mai Girma da kuma larabci
Abh Amr Al-basry ya kasance mai Gaskiya, mai Zuhudu, Mai Amana, mai yawan riko da Addini
An haifeshi a garin Makkah a shekara ta sittin da shida 68 bayan Hijrah.
An haifi Al-imam Abu Amr Al-basry a garin makkah, ya rayu a garin Basrah, ya Rasu a garin kufa.
Abu amr al-basry ya rasu a garin kufah, sai dai anyi sabani akan shekarar da ya rasu, wasu sukace ya rasu a shekara ta 154 bayan Hijrah, wasu sukace a shekara ta 155 bayan Hijrah, wasu sukace a shekara ta 157 bayan Hijrah, mafi nisan abunda aka fada akan shekarar da ya rasu itace shekara ta 158 bayan Hijrah.
Amma kuma maganar mafi yawan maluma itace ya rasu a shekara ta 154 bayan Hijrah, رحمه الله رحمة واسعة
2- SUWAYE MALAMAN AL-IMAM ABU AMR AL-BASRY
Al-imam Abu Amr Al-basry yafi kowa yawan Maluma daga cikin القُراء السبعة
Ga kadan daga Cikin Maluman shi:-
1- Anas ibn Malik رضي الله عنه
2- Hasanul-basriy
3- Humaid ibn 'Kais Al-a'araj
4- Sa'id ibn Jubair
5- Shaibah ibn nisah
6- Asim ibn Abin-najud Al-kufiy القارئ
7- Abdullahi ibn kathir Al-makky القارئ
8- Ada'u ibn Abi Rabah
9- Ikrimah Maula ibn Abbas رضي الله عنهما
10- mujahid ibn Jabr
Nan wasu ne kadan daga cikin maluman Abu Amr Al-basry da yayi karatu a gunsu baki-da-baki wasu kuma ta hanyar sauraro (سَمَاعًا)
3- MAGANAR MALAMAI AKAN ABU AMR AL-BASRY
Duk wanda ya tara wadannan ilmuka da kuma dabi'u na gari kamar yadda Abu Amr Al-basry ya tarasu dole ya samu yabo na kwarai daga malamai masana addini
Ga kadan daga Cikin Abubuwan da malamai suka Fada game da shi (Abu Amr Al-basry )
Abu Ubaidah yace:- Abu Amr Al-basry Ya dorawa kanshi cewa duk bayan kwana uku sai yayi saukar Al-Qur'ani Mai Girma.
Al-asma'iy yace:- Ban taba ganin wanda yafi abu Amr ilimi ba bayan wucewar shi.
Al-asma'iy yace:- Abu Amr yace min: "Da nasan yadda zanyi in kwashi ilimin dake kirjina in zubashi a kirjinka da nayi haka, Hakika na haddace ilmuka da dama da suka shafi ilmukan Al-Qur'ani wanda yakai da za'a Rubutasu Al-a'amash ( سليمان بن مهران الأعمَش) Bazai iya Daukar su ba, Da ba don Bazai yiyu inyi karatu ba sai da abunda magabata suka karanta Na Qur'ani (Qira'o'i) Da nayi karatu kala kaza da kala kaza! " Ya anbaci wasu harrufa daban na karatu.
Al-a'amash yace:- Wata rana Al-Hasanul-basriy ya zo zai wuce ta wurin Halkar Abu Amr ya isko mutane sunyi cikar kwari sun taru sun Dukufa ba abunda sukeyi illa karatu, sai Hasanul-basriy ya tambaya yace: wanene mai wannan Halkar? Sai akace dashi : Abu Amr ne, sai yace: لا إله إلا الله saura kiris maluma sun zamo iyayen jigi, Duk daukakar da ba'a Yimata ginshiki da katanga da ilimi ba to Kaskanci ne Karshenta".
SUFYAN IBN UYAINAH YACE : Nayi mafarkin Annabi صلى الله عليه وسلم sai na ce da manzon Allah صلى الله عليه وسلم : ya manzon Allah, Nau'i-Nau'i Na Qira'o'i sun Yawaita a gareni, Da Qira'ar wa kake umarta ta inyi karatu? Sai Annabi صلى الله عليه وسلم yace dashi : Da Qira'ar Abu Amr ibn Al-ala'.
Al-imam Ahmad ibn Hanbal yace: Qira'ar Abu Amr itace Mafi soyuwar Qira'a a gareni, Abu Amr yayi karatu ga ibn kathir da Mujahid da sa'id ibn Jubair, Su kuma sunyi karatu da ibn Abbas رضي الله عنهما shi kuma yayi karatu ga Ubayyu ibn ka'ab رضي الله عنه، shi kuma ubayyu yayi karatu ga Annabi صلى الله عليه وسلم.
Ibn mujahid yace: Malamai sun bamu labari daga Wahab ibn Jarir yace : Shu'ubah ( شعبة ابن الحجاج البصري) yace dani : Kayi riko da Qira'ar Abu Amr Domin Zata Kasance is'nadi (Abun riko) ga mutane.
IBN AL-JAZARIY YACE: Hakika abunda Shu'ubah ya fada ya Tabbata, Domin Kuwa Qira'ar da mafi yawan mutane suke karatu da ita a yau (yana nufin zamaninshi da yake wannan Maganar) a a garin Sham da Hijaz da Yemen da Misra itace Qira'ar Abu Amr al-basry, yana ma da wahala yana koya Qur'ani bada Qira'ar shi ba, musamman A bangaren فرش الحروف ( ban-bancin Hadaka na Qira'o'i) Duk da cewa suna sabawa a bangaren الأصول ( banbancin daidaiku na Qira'o'i), mutanen Sham Sun kasance suna Karatu da Qira'ar IBN AMIR tun zamanin ibn Amir Har zuwa wuraren shekara ta dari biyar 500 bayan Hijrah, Sai suka bar Karatu da Qira'ar ibn Amir din, saboda wani daga cikin Malamai yazo sham daga Iraq, ya cigaba da karantar da Mutane Qira'ar Abu Amr A masallacin AL-UMAWIY, mutane kuwa suka taru a wajenshi ana koyon wannan Qira'ar, wannan Qira'ar ta shahara a wannan Garin, ya kuma dade yana koyar dasu tsawon Shekaru, IBN AL-JAZARIY Yace wannan shine labarin da ya zomin dangane da sanadin barin Qira'ar Ibn Amir da mutanen sham sukayi suka koma suna Karatu da Qira'ar Abu Amr, idan ba wannan ba kuma Bansan sanadin da yasa suka barta ba, IBN AL-JAZARIY yace ina kirga wannan a daya daga cikin Karamomin Shu'ubah.
ABU AMR AL-ASADIY YACE :- A lokacin da labarin Rasuwar Abu Amr yazomin naje wurin Yayanshi na yimusu ta'aziyyar rasuwarshi, ina wurin sai YUNUS IBN HABIB yazo yace dasu (yayan abu Amr): muna yimuku Ta'aziyya haka kuma muna yiwa kanmu Ta'aziyya ta wanda bamu taba ganin irinshi ba a wannan zamani (yana nufin Abu Amr), yace : wallahi da za'a Rabawa mutane 100 Ilimin Abu Amru da Zuhudun shi Da duk sun kasance Malamai kuma masu Zuhudu, Wallahi da Annabi صلى الله عليه وسلم zaiga (Abu Amr) Da yayi farin ciki Dashi saboda yadda yake.
Wannan shine wani yanki daga cikin maganar maluma akan Abu Amr da rayuwar shi
والله أعلم
4- SUWAYE DALIBAN AL-IMAM ABU AMR AL-BASRY
Haka Kuma idan muka dawo ta gefen Daliban shi zamu fahimci cewa Al-imam Abu Amr Al-basry yanada dalibai masu dinbin yawa duba da lokacin da ya rayu lokaci ne na neman ilimi da yadashi.
Ga kadan daga Cikin Daliban shi
1- Ahmad ibn musa Al-lu'ulu'iy
2- Hussain ibn Ali Al-ju'ufiy
3- kharijah ibn mus'ab
4- khalid ibn Jabalah Al-yashkuriy
5- Sahl ibn Yusuf
6- Abdulrahim ibn musa
7- Abdullahi ibn Al-mubarak
8- Abdulmalik ibn Kuraib Al-asmu'iy
9- ubaid ibn Akil
10- yahya ibn Al-mubarak Al-yazidiy ( يَحْيى اليَزِيدِيّ)
Kadan kenan daga cikin Daliban Al-imam Abu Amr al-basry
5- TAKAITACCEN BAYANI AKAN QIRA'AR AL-IMAM ABU AMR AL-BASRY
Qira'ar Abu Amr Al-basry dayace daga cikin Qira'o'in Al-Qur'ani mai girma kuma itace ta uku 3 a jerin Qira'o'in, daga Qira'ar Al-imam Nafi'u sai Qira'ar Al-imam ibn kathir sai Qira'ar Abu Amr Al-basry.
AL-IMAM AHMAD IBN HAMBAL yace: Qira'ar Abu Amr itace Mafi soyuwar Qira'a a gareni, Abu Amr yayi karatu ga ibn kathir da Mujahid da sa'id ibn Jubair, Su kuma sunyi karatu da ibn Abbas رضي الله عنهما shi kuma yayi karatu ga Ubayyu ibn ka'ab رضي الله عنه، shi kuma ubayyu yayi karatu ga Annabi صلى الله عليه وسلم.
QIRA'AR Abu Amr tanada riwayoyi biyu kamar yadda sauran Qira'o'i suke da biyu-biyu, Ga su kamar haka
1- Riwayar Abu umar Hafs Al-duriy 150-246A.H
2- Riwayar Abu shu'aib Salih ibn Ziyad As-susiy, wanda ya rasu a shekara ta 261A.H
GA WANI BAYANI MAI MUHIMMANCI DA YA KAMATA MU SANI
👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇
mu sani cewa Duriy da Susiy Basuyi Karatu Kaitsaye (Baki da baki) Ga Abu Amr ba, sunyi karatu ne ga Yahya ibn Al-mubarak Al-yazidiy ( يَحْيَى اليَزِيدي) wanda Imamus-shadibiy yake cewa Game da shi :
= أَفَاضَ عَلى يَحْيَى اليَزِيديِّ سَيْبَهُ
فَأَصْبَحَ بِالعَذْبِ الفُرَاتِ مُعَلَّلا
= أبُو عُمَرَ الدُّوري وَصَالِحُهمْ أبو
شُعَيبٍ هُو السُّوسِيُّ عَنهُ تَقبَّلا
Fassara
= Abu Amr Al-basry ya kwaranyawa yahyal-yazidiyyi Baiwarshi ( iliminshi) yahya ya kasance kosasshe saboda ingantaccen ilimin da ya kwnkwada daga Abu Amr.
= Abu umar Ad-dury da kuma salihu mai Alkunya Abu Shu'ai wanda shine Ake kira Susi, Sun karbi Qira'ar Abu Amr a gareshi (يَحْيَى اليَزِيديِّ).
Ma'ana dai Akwai wasida a tsakanin su da Abu Amr
Nayi bayani a rubutu na na farko cewa
Wadanda ake Jinginawa riwayoyi (Masu Riwaya) Sun kasu gida uku
1- akwai wadanda sukayi karatu baki da baki ga QARI'AI da ake jinginawa riwayarsu zuwa garesu kamar
- Qalun da warsh sunyi karatu baki da baki ga Nafi'u
2- Akwai wadanda A tsakaninsu da QARI'AN akwai wasidar Mutun Daya kamar
- Dury da susi Sunyi karatu ga Yahyal Yazidiyyi shi kuma yahya yayi karatu ga Abu Amr Al-basry
-Kamar Khalaf da khallad Sunyi karatu ga Sulaim shi kuma sulaim Yayi Karatu Ga Hamzah
3- Akwai wadanda akwai fiye da mutun daya a tsakaninsu da QARI'IN DA sukayi riwaya a gareshi kamar
- Bazzi da Qumbul basuyi karatu kai tsaye ga ibn kathir ba Akwai fiye da mutun daya a tsakanin su
Abun da yasa hakan ta faru shine
A lokacin da wannan ilimin na riwayoyi yayi yawa ya fadada riwayoyin sunyi yawa Kasancewar kowane Qari'i yanada dalibai masu dinbin yawa kuma kowane daga cikin su yana jingina riwayar shi zuwaga wannan Qari'in
Sai akayi niyyar Takaita Riwayoyin Akace kowane QARI'I zaa fitar da mutun biyu daga cikin Rawiyanshi (Dalibanshi) Wadanda sukafi kwarewa da kuma tsoron Allah Da tsantseni domin a jingina riwayar shi zuwa garesu
Sai a bincika Idan an samu wanda ya cika sharudan daga cikin Daliban QARI'IN, haka kuwa akayi Zabin Ya fada Ga Duriy da Susi sai aka aka cigaba da jingina Qira'ar Abu Amr Al-basry zuwa garesu, Riwayar su kuma ake jinginata kai tsaye zuwa gareshi (Abu Amr Al-basry) Sabanin asalin Malaminsu ( yahyal-yazidiyyi)
Wannan shine Ma'anar Fadar Shadibiyy
تَخَيرَهم نُقَّادُهُم كلَّ بَارِعٍ
وَلَيسَ عَلى قُرءَانِه مُتَأَكِّلا
Adadin Ayoyin Qur'ani na wannan Qira'ar 6214
An sanya adadin Al-madany Al-auwal ( wato tsarin Kirga Ayoyin Al-madany na farko) dama tsarin Qirga Ayoyin Qur'ani akwai
المَدَني الأول
المدني الثاني
Akwai na makkah da sham da kufa da Basrah,
جَعلتُ المَدينِي أَولاً ثم ءاخِرا
وَمَكٍ إلى شَامِِ وكوفٍ إلى بَصْري
Haka Shadibiyy yace a cikin littafinshi ناظمة الزهر في عد آي السور
عد المدني الأول
Shine kafatanin Mutanen basrah ke aiki dashi a mushaf na Abu Amr da ya'akub
Adadin ayoyin su sune Dubu shida da dari biyu da sha hudu 6214
RAMZIN QIRA'AR ABU AMR AL-BASRY
Al-imam As-shadibiy ya yiwa Qira'ar Abu Amr Ramzi ( wato alamar da zai rika yin nuni akan Qira'ar Abu Amr da ita), Ramzin shine
HUDDI (حُطِّي)
wato idan akaga Ramzi na harafin ح a cikin Shadibiyyah to yana nuni ne akan Abu Amr Al-basry
Idan akaga Ramzi na harafin ط yana nufin Duri an Abi Amr
Idan akaga Ramzi na harafin ي to yana nufin Susi
Duk da cewa zai iya kiran kowane daga cikin su da sunanshi ko lakabinshi kai tsaye idan wazanin wakar ya bayar da damar yin haka.
Muna yin rubutun ne a takaice da sai mu bayar da misalin ko wanne daga cikin su, amma idan an koma Shadibiyyah zaa samu misallansu da yawa.
WASU KALMOMI DA ABU AMR AL-BASRY YA KEBANTA DASU DAGA CIKIN QARI'AI 10
Wannan babin kuma zai yi muna magana akan wasu kalmomi da Qira'ar Abu Amr ta sabawa sauran Qira'o'i a wurin Fadar su.
Gasu kamar haka:-
Abun lura a nan shine:- Harufan da nayiwa wasali su nikeso inyi nuni akansu da kuma Haruffan da na canjawa digo,
Zan rubuta kalmar da ya sabawa Qira'o'i akanta in kuma biyota da wasu kalmomi ta yadda za'a fahimci ayar da nike nufi,
Wata kalmar kuwa ita kadai zan kawo ina nufin Duk inda tazo a cikin Qurani mai Girma
👇👇👇
1- Duk inda wadannan Kalmomin sukazo a Al-Qur'ani Abu Amr yana karantasu tareda Daure harafin Ra'un رْ da ke cikinsu Ga Kalmomin
يامُرْكم يامُرْهم تامُرْهم ينصُرْكم يشعِرْكم
Haka kuma yana daure Harafin Hamza ءْ a wannan بارِئْكم
Sai dai riwayoyin shi biyu (Dury da susi) sunada sabanin fuskoki a wadannan Haruffan, a nemi littafai domin neman karin bayani
2- وإنه للحق من ربك وما الله بغــٰفل عما يَعملون
3- ويسئلونك ماذا ينفقون قل العفوُ
4- لا تُفْتَحُ لهم أبواب السماء ولا يدخلون الجنة
5- أُبْلِغُكم duk inda tazo
6- نغفر لكم خَطَـــٰـــيَــــٰــكُم سنزيد المحسنين
7- مما خَطَـــٰـــيَــــٰــهُم أغرقوا فأدخلوا نارا
8- أن يَقولوا يوم القيامة إنا كنا عن هذا غفلين
9- أو يَقولوا إنما أشرك ءباؤنا من قبل
10- وما نرىك اتبعك إلا الذين هم أراذلنا بادئَ الرأي
11- قلن حــٰشَا لله su uku, tareda yin madda ga Harafin ش duk da cewa ba yadda na rubutashi ake rubutashi a Qur'ani ba anayin Ilhakin Harafin Madda ne a wurin ش ٰ
12- ألا يَتخذوا من دوني وكيلا
13- وكان له ثُمْرٌ فقال لصاحبه
14- وأحيط بثُمْرِه فأصبح يقلب كفيه
15- قالوا إن هَــٰذَيْنِ لسحران yana daure ya'un يْ duk da cewa ba yadda na rubuta ta ake rubuta ta Qur'ani ba ana yin ilhakin ta ne
16- فاْجْمَعُوا كيدكم ثم ائتوا صفا
17- يوم نَنفُخ في الصور ونحشر المجرمين
18- وما عند الله خير وأبقى أفلا يَعقلون
19- إن الله كان بما يَعملون خبيرا (2). سورة الأحزاب
20- وكان الله بما يَعملون بصيرا () إذ جاءوكم من فوقكم..
21- جنت عدن يُدخَلونها يحلون فيها
22- كذلك يُجزَىٰ كُلُّ كفور
23- الشيطـن سول لهم وأُمْلِيَ لهم
24- من بعد عن أظفركم عليهم وكان الله بما يَعملون بصيرا ()
25- والذين ءامنوا وَأََتْبَعْنَـــٰــهُم ذُرِّيَّــــٰـــتِهم بإيمان
25- وقد أُخِذَ مِيثَـــٰــقُكم إن كنتم مؤمنين
26- فأصدق وَأَكُونَ من الصدقين () ولن يؤخر الله نفسا...
27- وإذا الرسل وُقِّتَت
28- بل يُؤثرون الحيوة الدنيا
Yadda na rubuta wadannan Kalmomin abu Amr ne kadai ke karantawa haka, kar a manta da sharadin da na bayar cewa Wurin wasulla ne da Digagga sabanin yake
والله أعلم
A Nemi littafan da sukayi magana akan Wannan Riwayar domin neman karin bayani ta yiyu kila akwai abunda ya kamata mu saka bamu saka ba.
Anan zamu tsaya sai a taremu a rubutu na gaba inda zaa jimu da Bayani akan Riwayar Dury An abi Amr Al-basry insha Allah
JAN HANKALI
👇👇👇👇
Duk wanda Zaiyi sharing ko Kwafi Na wannan Rubutun nawa To ya yi Sharing Dinshi A yadda Na Rubutashi Kar ya kara komai kuma Kar ya canja komai abar shi yadda nayishi
Duk wanda yakeda Taaliki ko gyara Ko shawara ko Mulahaza akan Wannan Rubutun to ya atuntubeni nizan gyara Da kaina Amma Kar A canja Min rubutu.
Ga lambar da zaa tuntubeni da ita +2348034468543
✍️WANDA YA RUBUTA
Habibu Muhammad Shugaba
+2348034468543
Tuesday
01-01-1443
10-08-2021