Monday, 24 January 2022

TARIHIN GONI MUHAMMAD KABIR YA'AQUB KANO

TARIHIN GONI MUHAMMAD KABIR YA'AQUB KANO

Rubutawa: Aminu Aliyu Sakwaya

FARKON RAYUWA
An haifeshi a 1966 a unguwar Yan awaki da ke birnin Kano.
Mahaifinsa ya kasance malami, mahaddacin Alkur'ani mai girma.
Ya yi karatu a wajen mahaifinsa da kuma kawunsa Mallam Garba, daga nan ya ci gaba a wajen Mallam Shu'aib dan Ringim bayan rasuwar mahaifinsa.
A 1979 mahaifinsa ya kai shi Maiduguri tsangayar Goni Adam dan Dakaso inda a nan ya kammala haddar Alkur'ani mai girma cikin kananan shekaru.
Daga nan ya shiga makarantun ilimi a nan Maiduri ya ci gaba da neman ilimin addinin musulunci.
Ya koyi ilimin tajwidi a wajen Goni Habu a Maiduguri, inda ya karanta littafin Hidayatul Murid da wasu littafan a wajensa.
MUSABAQA
1987 Borno - Ya yi musabakar izu sittin a ckin kwaryar birnin Maiduguri inda ya yi na uku, da aka hada da sauran kauyuka (kila ta zone) sai ya yi na biyar.
(Bai samu wakilci zuwa Jaha ba).
1987 Kano - Ya dawo gida hutu bayan kammala musabakar Borno, a Kano kuma lokacin ba a gama musabaka ba. Ya yi musabakar izu sittin a kwaryar birnin Kano inda ya yi na biyu a matakin karamar hukuma Kano Municpal.
1st: Gwani Nasir Abdullahi
2nd: Goni Kabir Ya'aqub
3rd: Gwani Lawi Gwani Dan Zarga
A MATAKIN JAHA KUMA:
1st: Gwani Nasiru Abdullahi
2nd: Sheikh Ja'afar Mahmud Adam
3rd:Gwani Lawi Gwani Dan Zarga
4th: Goni Kabir Ya'aqub
1988 - Kano - Ya sake na hudu a matakin Jaha
1989 Kano - Ya yi na daya a matakin Jaha
WADANDA SUKA WAKILCI KANO A WANNAN SHEKARAR A MUSABAKAR KASA A BAUCHI SU NE:
60 da Tafsiri: Sheikh Alkali Jibril Muhammad Mustapha Birnin Kudu
60 Hizb: Goni Kabir Ya'qub
40 Hizb: Goni Muhammad Khamis Umar
20 Hizb: Goni Abdul'aziz Hussain Akarami
10 Hizb: Mallam Auwal Abdulmumin
2 Hizb : Mallam Muhammad Tijjani Lawan
BANGAREN MATA:
Gwana Karimatu Sahalu - 30 Hizb
Maryam Ibrahim Kafin Hausa - Allah Ya mata rahama
Rumasa'u Shehu Ibrahim.
MUSABAKAR KASA A BAUCHI 1990
A matakin kasa, sai Mallam Jibril Muhammad Mustapha da Goni Kabir Ya'aqub suka samu nasarar mataki na daya, izu sittin da tafsir (Gwarzon Shekara) da izu sittin kenan. Sai dai ba su samu wakiltar Najeriya a musabakar duniya da ke Saudiyya ba sakamakon fara yakin tekun Fasha (Gulf War).
1ST POSITIONS WINNERS - 1990 BAUCHI NATIONAL MUSABAQAH
60 Hizb & Tafseer: Jibril Muhammad Mustapha Kano State
60 Hizb: Muhammad Kabir Ya'aqub Kano State
40 Hizb: Alghali Bishara Borno State
20 Hizb: Khamis Balarabe Plateau State - Allah Ya masa rahama
10 Hizb: Nasir Abdurrahman Funtua Katsina State
ALKALANCIN MUSABAQA
1998 - An nada shi alkalin musabakar a Jahar Kano a matakin kananan hukumomi
2003-2007: Ya yi alkalanci a musabakar kasa ta Najeriya bangaren maza
2007 - An zabeshi daga Najeriya inda ya yi alkalanci a musabakar duniya ta Sarki Abdul'aziz da ake gabatarwa a Saudiyya duk shekara.
NADIN GONI
2007 - Goni Abdullahi Borno ya nada shi Goni daga shawarin malaminsa Goni Adam dan Dakaso.
KARATUN QIRA'AT
Alhaji Ado Dan Dawaki ya dauki nauyinsa inda ya tafi Misra ya yi karatun Qira'at a wajen Sheikh Ridha Salim shekara daya.
Ya samu International Scholarship karkashin Gwamnar Jahar Kano na mulkin soja Kanar Idris Garba inda ya koma Misra ya shekara uku a Ma'ahad Qira'at bangaren Aliyat-Qira'at, ya kuma samu ijaza a Qira'o'i goma wajen Sheikh Saleem Ridha.
KARATUN ZAMANI
2010 - Ya kammala N.C.E a Sa'adatu Rimi College of Education, Kano
2013 - 2017: B.Ed Islamic Education - Northwest University, Kano
2019 2021: Master's Degree - Islamic Studies - Bayero University, Kano
2021 - Date - Ya fara Ph.D a Bayero University, Kano
MAJALISIN KARANTARWA
Babban majlisin da ake koyon karatun Alkur'ani da Ada'i da Qira'at da tadribin yan musabaqah dake unguwar Dorayi cikin birnin Kano.
Duk Asabar da Lahadi bayan sallar Asuba Goni Kabir na karantarwa a wannan majalisi - Allah Ya saka masa da alheri.
WASU DAGA CIKIN TSOFFIN MAHALARTA WANNAN MAJALISI
Zai yi wuya ka samu mutum daya da ya kasance zakara a musabaqar Jahar Kano da kuma kewayenta face Goni Kabir ya karantar da shi, ko kuma daliban Goni Kabir sun karantar da shi.
Lalle mafiya kyawun karatun Alkur'ani a Kano da kuma kewayanta za ka samu sun fa'idanta da kwarewa da baiwa da gogewa da iya karatu da rerawa da kuma kyan ada'i da Qira'at da Allah Yai wa Goni Kabir Ya'aqub.
Ana daukarsa Jaha-Jaha domin ya yi wa dalibai da yan musabaqah tadribi na yadda ake karatun Alkur'ani mai girma.
Ga wasu daga cikin zakaru a musabakar Alkurani mai girma da wannan majalisi ya yaye;
Mazidu Adam Shu'aib - Gwarzon Shekara 2003 Nasarawa
Zubair Hamza Dahir - Gwarzon Shekara 2005 Kano
Kabir Abubakar Musa - Gwarzon Shekara da Duniya 2013 Zamfara
Jamilu Lawan - 2004 Kebbi 40 Hizb 1st
Aminu Hassan - 2009 Edo 60 Hizb 1st
Mukhtar Barnoma - Gwarzon Shekara 2009 Edo
Idris Abdulkadir - 2006 Bauchi 60 Hizb 1st
Shamsu Lawan - 2007 -40H-2nd | 2010 -60H-5th | 2014-Tafsir-4th | Kuwait
Abdullahi Aliyu - 2013 Zamfara 60 Hizb - 1st
Mulkhtar Umar
Faruq Goni Kabir Ya'aqub - Ya sha wakiltar Kano a musabakar kasa
Da sauran dubunnan mutane.
Allah Ya sakawa Mallam da alheri Ya karbi aiyukansa na alkhairi Ya kyautata bayansa.

Littafin da aka duba: Littafin Tatawwur na Dr. Rufa'i Uba Hamza Gabari da sauran takardun bincike

Saturday, 14 August 2021

Biography of Goni Tahir Maiduguri

Biography of Goni Tahir Goni Idris Borno

Read the post on Facebook here

Compiled by Aminu Sakwaya

Tahir Goni Idris Anna'im was born in 1977 at Gombe State, but his origin is from Borno.
Goni brought up and had his local tsangaya Quranic school in Borno. He memorized the Glorious Quran at younger age and studied Tajweed and Qira'at from various prominent and well known Quranic reciters in Borno before he went abroad.
Goni graduated from Al-Azhar University 2006 – Faculty of Shari’ah & Law. While studying Shari’ah at Egypt, he enrolled in one of the Qur’anic schools and had the privilege of getting Ijaza in Qira’at al-ashra assugra wal kubra( the Ten various schools/methodologies of reciting the Glorious Qur’an).
From Egypt, he proceed to Islamic University of Madina and graduated in 2014 with Master Degree in Qira’at – Faculty of Qur’anic Sciences.
Goni then went to African University, Sudan and started his Ph.D Degree.
In the field of musabaqa, Goni Tahir represented Nigeria at Saudi King Abdul'aziz Int'l Quran Competition in 1994 and came 1st in the memorization of 60 Hizb (second category).
He also participated in 2002 Dubai Int’l Holy Qur’an Award and won 4th.
Goni participated also at Misra Int’l Musabaqa and won 2nd.
Goni Tahir had been among the judges at 2011 King Abdul’aziz Int’l Musabaka – Saudi Arabia, 2012 Sudan International Musabaqa, 2013 Kuwait International Holy Qur’an Award and 2018 Dubai International Holy Quran Award/Musabakatu Shaikha Fatima Bint Mubarak ( for Females).
In Nigeria, Goni Tahir formerly, was among the panel of judges in Nigerian National Qur’anic Recitation Competition from 2007 to 2013.
Goni was blessed with retentive memory and this had been proved when he read the entire Qur’an by heart to Gwani Rufa’i in preparation to represent Nigeria in 2002 and make no repetition throughout except one WORD in Surat al-A’raf.
Goni recorded the Glorious Qur’an – Riwayati Hafs – when he was at Egypt and lectured at University of Maiduguri.

Biography of Gwani Sadiq Gusau

Biography of Gwani Sadiq Gusau

By Aminu Sakwaya

Read the post on Facebook here

Gwani Sadiq was from Gusau, Zamfara State, Nigeria. Born at Tafki Tara, Kebbi State. He memorized the Glorious Qur'an in the hand of his father. He later travelled to Gusau, Sheikh Sunusi Balarabe Zawiyya, to pursue Qur'anic knowledge.

He was among the top Nigerian Qur'anic reciters.
In 1994, Gwani Sadiq represented Sokoto State in the National Quranic Recitation Competition and won 11th position in the memorization of 60 Hizb (second category without Tafsir). He contested with Riwayati Warsh.
In 1995, he bagged 3rd position and won 1st in 1996 (in the same category, i.e 60 Hizb ) where he contested with Riwayati Hafs.
He represented Nigeria at King Fahad International Qur'anic Competition, Makkah, where he got 1st position in the 2nd category(60 Hizb),making him the third amongst the 5 Nigerians that attained this rank( others being Gwani Umar Al-Bashir, Gwani Tahir Idris, Gwani Abdurrahman Durma, and recently, Idris Abubakar,all from Borno State, Nigeria). This was in the year 1996/1997. الله اكبر Other Nigerian participants during the same year are Sheikh Abubakar Rabah Kebbi (Tafsir), Gwani Fadlu Kura Kano(40 Hizb), Dr Mansur Yelwa Bauchi(20 Hizb) and Isma'il Salis Katsina (10 Hizb).
He was a judge( for correction) in Nigerian National Qur'anic Recitation Competition from 2001 to 2013, and reappointed from 2018 to date.
He memorized Shatibiyya, Al-Durrah and on-going Taiyibah An-Nashr (2013 interview at Wisal Hausa Tv)
In 2011, he was chosen to be among the panel of Judges at King Fahd International Holy Quran Competition, Makkah and assigned to correct (and later to read the questions as well) the contestants.
Yana da yawan murmushi da faran-faran da jama'a ' he smiles alot'.
He had Jumu'at Masjid and delivered annual Ramadan Tafsir there.
He teaches many Fikh, Lugga and Qira'at at his school in Gusau.
Goni (in ji mutanen Borno) wrote a book on Tajweed and recorded complete Quran in Hafs, Warsh, Qalun and Khalaf.
Very soon, in sha Allah, the recorded version of 10 various Qira'at (20 Riwayat) will be launched by God's grace.
Takabbalallahu an shaikhina wa jazahullahu anna khairal jaza'